< Zabura 22 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
En Psalm Davids, till att föresjunga, om hindena som bittida jagad varder. Min Gud, min Gud, hvi hafver du öfvergifvit mig? Jag ryter; men min hjelp är fjerran.
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
Min Gud, om dagen ropar jag, så svarar du intet; och om nattena tiger jag ock intet.
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
Men du äst helig, du som bor ibland Israels lof.
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
Våre fäder hoppades uppå dig; och då de hoppades, halp du dem ut.
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
Till dig ropade de, och vordo hulpne; de hoppades på dig, och vordo icke till skam.
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
Men jag är en matk, och icke menniska; menniskors gabberi, och folks föraktelse.
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
Alle de som mig se, bespotta mig, gapa upp med munnen, och rista hufvudet:
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
Han klage det Herranom; han hjelpe honom ut, och undsätte honom, om han hafver lust till honom.
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
Ty du hafver dragit mig utu mitt moderlif; och vast min tröst, då jag än vid mine moders bröst låg.
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
På dig är jag kastad utaf moderlifvet; du äst min Gud, allt ifrå mine moders lif.
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
Var icke långt ifrå mig; ty ångest är hardt när; ty här är ingen hjelpare.
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
Store stutar hafva belagt mig; fete oxar hafva omhvärft mig.
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
De uppgapa med sin mun emot mig, såsom ett glupande och rytande lejon.
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
Jag är utgjuten såsom vatten; all min ben hafva skiljts åt; mitt hjerta i mitt lif är såsom ett smält vax.
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
Mina krafter äro borttorkade, såsom ett stycke af en potto; och min tunga lådar vid min gom, och du lägger mig uti dödsens stoft.
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
Ty hundar hafva kringhvärft mig, och de ondas rote hafver ställt sig omkring mig; mina händer och fötter hafva de genomborrat.
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
Jag måtte tälja all min ben; men de skåda och se sin lust på mig.
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
De byta min kläder emellan sig, och kasta lott om min klädnad.
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
Men du, Herre, var icke fjerran; min starkhet, skynda dig till att hjelpa mig.
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
Fria mina själ ifrå svärdet, mina ensamma ifrå hundarna.
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
Hjelp mig utu lejonens mun, och fria mig ifrån enhörningarna.
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
Jag vill predika ditt Namn minom brödrom; jag vill prisa dig i församlingene.
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
Lofver Herran, I som frukten honom; honom äre all Jacobs säd, och honom vörde all Israels säd.
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
Ty han hafver icke föraktat eller försmått dens fattiga eländhet; och icke förskylt sitt ansigte för honom; och då han ropade till honom, hörde han det.
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
Dig vill jag prisa, uti den stora församlingene; jag vill betala mitt löfte inför dem som frukta honom.
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
De elände skola äta, att de mätte varda; och de som efter Herran fråga, skola prisa honom; edart hjerta skall lefva evinnerliga.
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
Tänke derpå alla verldenes ändar, och omvände sig till Herran; och alla Hedningars slägter tillbedje för honom.
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
Herren hafver ett rike, och han råder ibland Hedningarna.
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
Alle fete på jordene skola äta, och tillbedja; för honom skola knäböja alle de som i stoft ligga, och de der med bekymmer lefva.
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
Han skall få ena säd, den honom tjenar; om Herran skall man förkunna intill barnabarn.
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
De skola, komma och predika hans rättfärdighet de folke, som födas skall, att han det gör.