< Zabura 22 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
¡ʼEL mío, ʼEL mío! ¿Por qué me desamparaste? ¿Por qué estás lejos de mi salvación y de las palabras de mi clamor?
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
ʼElohim mío, clamo de día, y no respondes, Y de noche, y no hay descanso para mí.
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
Pero Tú eres santo, ¡Tú, que moras entre las alabanzas de Israel!
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
En Ti confiaron nuestros antepasados. Confiaron, y Tú los libraste.
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
Clamaron a Ti, y fueron librados. Confiaron en Ti, y no fueron avergonzados.
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
Pero yo soy gusano y no hombre, Oprobio de los hombres y despreciado por el pueblo.
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
Todos los que me ven me escarnecen. Hacen una mueca con los labios. Menean la cabeza y dicen:
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
Se encomendó a Yavé. Líbrelo Él. Que Él lo rescate, Puesto que se complacía en Él.
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
Pero Tú eres el que me sacó del vientre. Me diste confianza aun cuando estaba a los pechos de mi madre.
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
A Ti fui entregado desde la matriz, Desde el vientre de mi madre Tú eres mi ʼEL.
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
No te alejes de Mí, porque la angustia está cerca, Porque no hay quien ayude.
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
Me rodearon muchos toros. Fuertes toros de Basán me rodearon.
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
Abren su boca contra mí Como león voraz y rugiente.
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
Soy derramado como aguas Y todos mis huesos se descoyuntan. Mi corazón se volvió como cera. Se derritió entre mis órganos.
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
Mi vigor está seco como tiesto Y mi lengua se pega a mis mandíbulas. ¡Me pones en el polvo de la muerte!
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
Perros me rodearon. Me cercó cuadrilla de perversos. Horadaron mis manos y mis pies.
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
Puedo contar todos mis huesos. Ellos me miran y me observan.
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
Reparten entre sí mis ropas, Y sobre mi túnica echan suertes.
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
Pero Tú, oh Yavé, ¡no te alejes! Fortaleza mía, ¡Apresúrate a socorrerme!
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
¡Libra de la espada el alma mía, Del poder del perro mi vida!
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
¡Sálvame de la boca del león Y de los cuernos de los toros salvajes! ¡Me has respondido!
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
Anunciaré tu Nombre a mis hermanos. En medio de la congregación te alabaré.
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
Los que temen a Yavé, alábenlo. Glorifíquenlo, toda la descendencia de Jacob, Y témanle, toda la descendencia de Israel,
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
Porque no menospreció ni aborreció el dolor del afligido, Ni de él ocultó su rostro, Sino cuando clamó a Él, Lo escuchó.
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
De Ti viene mi alabanza en la gran congregación. Cumpliré mis votos delante de los que te temen.
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
¡Los pobres comerán y serán saciados! ¡Alabarán a Yavé los que lo buscan! ¡Que su corazón viva para siempre!
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
Se acordarán y volverán a Yavé de todos los confines de la tierra, Y todas las familias de las naciones se postrarán delante de Ti.
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
Porque de Yavé es el reino, Y Él gobierna las naciones.
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
Comerán y se postrarán Todos los poderosos de la tierra, Los que bajan al polvo se postrarán ante Él, Los que no pueden conservar viva su alma.
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
Una futura generación le servirá. Esto se dirá de ʼAdonay hasta la próxima generación.
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
Acudirán y declararán su justicia, Anunciarán a pueblo que nacerá que Él hizo esto.

< Zabura 22 >