< Zabura 22 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
Moj Bog, moj Bog, zakaj si me zapustil? Zakaj si tako daleč proč od pomoči meni in od besed mojega vpitja?
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
Oh moj Bog, jokam podnevi, toda ti me ne uslišiš in v nočnem času in nisem tiho.
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
Toda ti si svet, oh ti, ki naseljuješ Izraelove hvalnice.
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
Naši očetje so zaupali vate. Zaupali so in si jih osvobodil.
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
Klicali so k tebi in so bili osvobojeni. Zaupali so vate in niso bili zbegani.
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
Toda jaz sem [škrlatni] črv in ne mož; graja ljudem in preziran od ljudstva.
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
Vsi, ki me vidijo, se mi smejijo do norčevanja. Namrdnejo ustnico [in] zmajujejo z glavo, rekoč:
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
»Zaupal je v Gospoda, da ga bo osvobodil. Naj ga reši, glede na to, da se je razveseljeval v njem.«
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
Toda ti si ta, ki me je potegnil iz maternice. Oblikoval si mi zaupanje, ko sem bil na prsih svoje matere.
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
Iz maternice sem bil vržen nate. Ti si moj Bog od trebuha moje matere.
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
Ne bodi daleč od mene, kajti stiska je blizu, kajti nikogar ni, da pomaga.
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
Obdalo me je mnogo bikov. Močni bašánski biki so me obdali naokoli.
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
S svojimi gobci so zevali vame, kakor ropa željan in rjoveč lev.
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
Izlit sem kakor voda in vse moje kosti so izpahnjene. Moje srce je podobno vosku, stopljeno je v sredi moje notranjosti.
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
Moja moč je izsušena kakor črepinja in moj jezik se lepi k mojim čeljustim in ti si me privedel v smrtni prah.
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
Kajti psi so me obdali. Zajel me je zbor zlobnih. Prebodli so moje roke in moja stopala.
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
Vse svoje kosti lahko razločim. Oni pa gledajo in strmijo vame.
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
Moje obleke si razdeljujejo med seboj in za mojo suknjo so metali žrebe.
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
Toda ti, oh Gospod, ne bodi daleč od mene. Oh moja moč, hiti, da mi pomagaš.
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
Osvobodi mojo dušo pred mečem, mojo ljubljeno pred močjo psa.
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
Reši me pred levjimi usti, kajti uslišal si me pred rogovi samorogov.
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
Tvoje ime bom oznanjal svojim bratom. Na sredi skupnosti te bom hvalil.
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
Vi, ki se bojite Gospoda, hvalite ga, vsi vi, seme Jakobovo, proslavite ga, in bojte se ga, vsi vi, seme Izraelovo.
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
Kajti ni zaničeval niti preziral stiske stiskanih niti svojega obraza ni skrival pred njim; toda ko je klical k njemu, je slišal.
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
Moja hvala v veliki skupnosti bo o tebi. Svoje zaobljube bom izpolnil pred tistimi, ki se ga bojijo.
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
Krotki bodo jedli in bodo nasičeni. Hvalili bodo Gospoda [tisti], ki ga iščejo. Vaše srce bo živelo na veke.
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
Vsi konci zemlje se bodo spomnili in obrnili h Gospodu in vsa sorodstva narodov bodo oboževala pred teboj.
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
Kajti kraljestvo je Gospodovo in on je voditelj med narodi.
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
Vsi tisti, ki so na zemlji obilni, bodo jedli in oboževali. Vsi tisti, ki gredo dol v prah, se bodo poklonili pred njim, svoje lastne duše pa nihče ne more ohraniti žive.
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
Seme mu bo služilo; to bo šteto h Gospodu za rod.
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
Prišli bodo in oznanjali bodo njegovo pravičnost ljudem, ki bodo rojeni, da je on to storil.

< Zabura 22 >