< Zabura 22 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
برای سالار مغنیان بر غزاله صبح. مزمور داود ای خدای من، ای خدای من، چرا مراترک کرده‌ای و از نجات من و سخنان فریادم دور هستی؟۱
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
‌ای خدای من در روز می خوانم و مرا اجابت نمی کنی. در شب نیز و مراخاموشی نیست.۲
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
و اما تو قدوس هستی، ای که بر تسبیحات اسرائیل نشسته‌ای.۳
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
پدران ما بر توتوکل داشتند. بر تو توکل داشتند و ایشان راخلاصی دادی.۴
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
نزد تو فریاد برآوردند و رهایی یافتند. بر تو توکل داشتند، پس خجل نشدند.۵
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
و اما من کرم هستم و انسان نی. عار آدمیان هستم و حقیر شمرده شده قوم.۶
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
هرکه مرا بیند به من استهزا می‌کند. لبهای خود را باز می‌کنند وسرهای خود را می‌جنبانند (و می‌گویند):۷
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
«برخداوند توکل کن پس او را خلاصی بدهد. او رابرهاند چونکه به وی رغبت می‌دارد.»۸
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
زیرا که تومرا از شکم بیرون آوردی؛ وقتی که بر آغوش مادر خود بودم مرا مطمئن ساختی.۹
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
از رحم برتو انداخته شدم. از شکم مادرم خدای من توهستی.۱۰
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
از من دور مباش زیرا تنگی نزدیک است. و کسی نیست که مدد کند.۱۱
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
گاوان نربسیار دور مرا گرفته‌اند. زورمندان باشان مرااحاطه کرده‌اند.۱۲
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
دهان خود را بر من باز کردند، مثل شیر درنده غران.۱۳
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
مثل آب ریخته شده‌ام. وهمه استخوانهایم از هم گسیخته. دلم مثل موم گردیده، در میان احشایم گداخته شده است.۱۴
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
قوت من مثل سفال خشک شده و زبانم به کامم چسبیده. و مرا به خاک موت نهاده‌ای.۱۵
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
زیراسگان دور مرا گرفته‌اند. جماعت اشرار مرا احاطه کرده، دستها و پایهای مرا سفته‌اند.۱۶
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
همه استخوانهای خود را می‌شمارم. ایشان به من چشم دوخته، می‌نگرند.۱۷
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
رخت مرا در میان خود تقسیم کردند. و بر لباس من قرعه انداختند.۱۸
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
اما تو‌ای خداوند دور مباش. ای قوت من برای نصرت من شتاب کن.۱۹
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
جان مرا از شمشیرخلاص کن. و یگانه مرا از دست سگان.۲۰
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
مرا ازدهان شیر خلاصی ده. ای که از میان شاخهای گاووحشی مرا اجابت کرده‌ای.۲۱
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
نام تو را به برادران خود اعلام خواهم کرد. در میان جماعت تو راتسبیح خواهم خواند.۲۲
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
‌ای ترسندگان خداوند او را حمد گویید. تمام ذریت یعقوب او را تمجید نمایید. و جمیع ذریت اسرائیل از وی بترسید.۲۳
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
زیرا مسکنت مسکین را حقیر و خوار نشمرده، و روی خود رااز او نپوشانیده است. و چون نزد وی فریاد برآورداو را اجابت فرمود.۲۴
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
تسبیح من در جماعت بزرگ از تو است. نذرهای خود را به حضورترسندگانت ادا خواهم نمود.۲۵
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
حلیمان غذاخورده، سیر خواهند شد. و طالبان خداوند او راتسبیح خواهند خواند. و دلهای شما زیست خواهد کرد تا ابدالاباد.۲۶
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
جمیع کرانه های زمین متذکر شده، بسوی خداوند بازگشت خواهندنمود. و همه قبایل امت‌ها به حضور تو سجده خواهند کرد.۲۷
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
زیرا سلطنت از آن خداونداست. و او بر امت‌ها مسلط است.۲۸
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
همه متمولان زمین غذا خورده، سجده خواهند کرد. وبه حضور وی هر‌که به خاک فرو می‌رود رکوع خواهد نمود. و کسی جان خود را زنده نخواهدساخت.۲۹
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
ذریتی او را عبادت خواهند کرد ودرباره خداوند طبقه بعد را اخبار خواهند نمود.۳۰
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
ایشان خواهند آمد و از عدالت او خبرخواهند داد، قومی را که متولد خواهند شد که اواین کار کرده است.۳۱

< Zabura 22 >