< Zabura 22 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
In finem, pro susceptione matutina. Psalmus David. [Deus, Deus meus, respice in me: quare me dereliquisti? longe a salute mea verba delictorum meorum.
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
Deus meus, clamabo per diem, et non exaudies; et nocte, et non ad insipientiam mihi.
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
Tu autem in sancto habitas, laus Israël.
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
In te speraverunt patres nostri; speraverunt, et liberasti eos.
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
Ad te clamaverunt, et salvi facti sunt; in te speraverunt, et non sunt confusi.
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
Ego autem sum vermis, et non homo; opprobrium hominum, et abjectio plebis.
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
Omnes videntes me deriserunt me; locuti sunt labiis, et moverunt caput.
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
Speravit in Domino, eripiat eum: salvum faciat eum, quoniam vult eum.
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
Quoniam tu es qui extraxisti me de ventre, spes mea ab uberibus matris meæ.
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
In te projectus sum ex utero; de ventre matris meæ Deus meus es tu:
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
ne discesseris a me, quoniam tribulatio proxima est, quoniam non est qui adjuvet.
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
Circumdederunt me vituli multi; tauri pingues obsederunt me.
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
Aperuerunt super me os suum, sicut leo rapiens et rugiens.
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
Sicut aqua effusus sum, et dispersa sunt omnia ossa mea: factum est cor meum tamquam cera liquescens in medio ventris mei.
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
Aruit tamquam testa virtus mea, et lingua mea adhæsit faucibus meis: et in pulverem mortis deduxisti me.
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
Quoniam circumdederunt me canes multi; concilium malignantium obsedit me. Foderunt manus meas et pedes meos;
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
dinumeraverunt omnia ossa mea. Ipsi vero consideraverunt et inspexerunt me.
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
Diviserunt sibi vestimenta mea, et super vestem meam miserunt sortem.
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
Tu autem, Domine, ne elongaveris auxilium tuum a me; ad defensionem meam conspice.
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
Erue a framea, Deus, animam meam, et de manu canis unicam meam.
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
Salva me ex ore leonis, et a cornibus unicornium humilitatem meam.
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
Narrabo nomen tuum fratribus meis; in medio ecclesiæ laudabo te.
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
Qui timetis Dominum, laudate eum; universum semen Jacob, glorificate eum.
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
Timeat eum omne semen Israël, quoniam non sprevit, neque despexit deprecationem pauperis, nec avertit faciem suam a me: et cum clamarem ad eum, exaudivit me.
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
Apud te laus mea in ecclesia magna; vota mea reddam in conspectu timentium eum.
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
Edent pauperes, et saturabuntur, et laudabunt Dominum qui requirunt eum: vivent corda eorum in sæculum sæculi.
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
Reminiscentur et convertentur ad Dominum universi fines terræ; et adorabunt in conspectu ejus universæ familiæ gentium:
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
quoniam Domini est regnum, et ipse dominabitur gentium.
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
Manducaverunt et adoraverunt omnes pingues terræ; in conspectu ejus cadent omnes qui descendunt in terram.
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
Et anima mea illi vivet; et semen meum serviet ipsi.
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
Annuntiabitur Domino generatio ventura; et annuntiabunt cæli justitiam ejus populo qui nascetur, quem fecit Dominus.]

< Zabura 22 >