< Zabura 22 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
למנצח על-אילת השחר מזמור לדוד ב אלי אלי למה עזבתני רחוק מישועתי דברי שאגתי
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
אלהי--אקרא יומם ולא תענה ולילה ולא-דמיה לי
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
ואתה קדוש-- יושב תהלות ישראל
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
בך בטחו אבתינו בטחו ותפלטמו
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
אליך זעקו ונמלטו בך בטחו ולא-בושו
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
ואנכי תולעת ולא-איש חרפת אדם ובזוי עם
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
כל-ראי ילעגו לי יפטירו בשפה יניעו ראש
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
גל אל-יהוה יפלטהו יצילהו כי חפץ בו
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
כי-אתה גחי מבטן מבטיחי על-שדי אמי
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
עליך השלכתי מרחם מבטן אמי אלי אתה
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
אל-תרחק ממני כי-צרה קרובה כי-אין עוזר
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
סבבוני פרים רבים אבירי בשן כתרוני
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
פצו עלי פיהם אריה טרף ושאג
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
כמים נשפכתי-- והתפרדו כל-עצמותי היה לבי כדונג נמס בתוך מעי
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
יבש כחרש כחי ולשוני מדבק מלקוחי ולעפר-מות תשפתני
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
כי סבבוני כלבים עדת מרעים הקיפוני כארי ידי ורגלי
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
אספר כל-עצמותי המה יביטו יראו-בי
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
יחלקו בגדי להם ועל-לבושי יפילו גורל
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
ואתה יהוה אל-תרחק אילותי לעזרתי חושה
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
הצילה מחרב נפשי מיד-כלב יחידתי
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
הושיעני מפי אריה ומקרני רמים עניתני
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
אספרה שמך לאחי בתוך קהל אהללך
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
יראי יהוה הללוהו-- כל-זרע יעקב כבדוהו וגורו ממנו כל-זרע ישראל
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
כי לא-בזה ולא שקץ ענות עני-- ולא-הסתיר פניו ממנו ובשועו אליו שמע
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
מאתך תהלתי בקהל רב--נדרי אשלם נגד יראיו
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
יאכלו ענוים וישבעו-- יהללו יהוה דרשיו יחי לבבכם לעד
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
יזכרו וישבו אל-יהוה-- כל-אפסי-ארץ וישתחוו לפניך כל-משפחות גוים
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
כי ליהוה המלוכה ומשל בגוים
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
אכלו וישתחוו כל-דשני-ארץ-- לפניו יכרעו כל-יורדי עפר ונפשו לא חיה
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
זרע יעבדנו יספר לאדני לדור
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
יבאו ויגידו צדקתו לעם נולד כי עשה

< Zabura 22 >