< Zabura 22 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
Pour la fin, pour le secours du matin, psaume de David. Dieu, mon Dieu, regardez-moi: pourquoi m’avez-vous délaissé? Les paroles de mes péchés sont loin de mon salut.
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
Mon Dieu, je crierai pendant le jour, et vous ne m’exaucerez pas: et pendant la nuit, et ce n’est point à moi une folie.
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
Mais vous, vous habitez dans un sanctuaire, vous la louange d’Israël.
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
C’est en vous qu’ont espéré nos pères: ils ont espéré, et vous les avez délivrés.
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
Vers vous ils ont crié et ils ont été sauvés: en vous ils ont espéré, et ils n’ont point été confondus.
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
Pour moi je suis un ver et non pas un homme; l’opprobre des hommes et l’abjection du peuple.
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
Tout ceux qui m’ont vu m’ont tourné en dérision: ils ont parlé du bout des lèvres, et ils ont secoué la tête.
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
Il a espéré dans le Seigneur, qu’il le délivre; qu’il le sauve, puisqu’il l’aime.
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
Cependant c’est vous qui m’avez tiré du sein de ma mère: vous êtes mon espérance depuis que je suçais les mamelles de ma mère.
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
C’est sur vous que j’ai été posé, en sortant de son sein; depuis que j’étais dans les entrailles de ma mère, vous êtes mon Dieu.
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
Ne vous éloignez pas de moi:
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
De jeunes taureaux en grand nombre m’ont environné; des taureaux gras m’ont assiégé.
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
Ils ont ouvert sur moi leur gueule comme un lion ravissant et rugissant.
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
Je me suis épanché comme de l’eau, et tous mes os se sont déboîtés. Mon cœur est devenu au dedans de moi comme une cire qui se fond.
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
Ma force s’est desséchée comme un têt, et ma langue s’est attachée à mon palais; et vous m’avez conduit à la poussière de la mort.
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
Parce que des chiens nombreux m’ont environné; un conseil de méchants m’a assiégé: Ils ont percé mes mains et mes pieds:
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
Ils ont compté tous mes os. Ils m’ont eux-mêmes considéré et regardé attentivement.
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
Ils se sont partagé mes vêtements, et sur ma robe ils ont jeté le sort.
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
Mais vous, Seigneur, n’éloignez pas votre secours de moi: voyez à ma défense.
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
Arrachez mon âme à l’épée à double tranchant; et mon unique de la main du chien.
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
Sauvez-moi de la gueule du lion; et ma faiblesse des cornes des licornes.
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
Je raconterai votre nom à mes frères; je vous louerai au milieu de l’assemblée.
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
Vous qui craignez le Seigneur, louez-le; race entière de Jacob, glorifiez-le:
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
Que toute la race d’Israël le craigne, parce qu’il n’a pas méprisé ni dédaigné la supplication du pauvre; Et qu’il n’a point détourné sa face de moi, et que lorsque je criais vers lui, il m’a exaucé.
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
Devant vous sera ma louange dans une grande assemblée: je rendrai mes vœux en présence de ceux qui le craignent.
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
Les pauvres mangeront et seront rassasiés; et ils loueront le Seigneur, ceux qui le recherchent; leurs cœurs vivront dans les siècles des siècles.
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
Tous les confins de la terre se souviendront du Seigneur et se convertiront à lui: Et toutes les familles des nations adoreront en sa présence.
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
Parce qu’au Seigneur appartient le règne; et que c’est lui qui dominera sur les nations.
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
Tous les riches de la terre ont mangé et ont adoré: en sa présence tomberont tous ceux qui descendent dans la terre.
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
Et mon âme vivra pour lui; et ma postérité le servira.
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
La génération qui doit venir sera annoncée au Seigneur; et les cieux annonceront sa justice au peuple qui naîtra, et qu’a fait le Seigneur.

< Zabura 22 >