< Zabura 22 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
Au maître de chant. Sur « Biche de l’aurore ». Psaume de David. Mon Dieu, mon Dieu, pourquoi m’as-tu abandonné? Je gémis, et le salut reste loin de moi!
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
Mon Dieu, je crie pendant le jour, et tu ne réponds pas; la nuit, et je n’ai pas de repos.
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
Pourtant tu es saint, tu habites parmi les hymnes d’Israël.
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
En toi se sont confiés nos pères; ils se sont confiés, et tu les as délivrés.
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
Ils ont crié vers toi, et ils ont été sauvés; ils se sont confiés en toi, et ils n’ont pas été confus.
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
Et moi, je suis un ver, et non un homme, l’opprobre des hommes et le rebut du peuple.
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
Tous ceux qui me voient se moquent de moi; ils ouvrent les lèvres, ils branlent la tête:
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
« Qu’il s’abandonne à Yahweh! Qu’il le sauve, qu’il le délivre, puisqu’il l’aime! »
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
Oui, c’est toi qui m’as tiré du sein maternel, qui m’as donné confiance sur les mamelles de ma mère.
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
Dès ma naissance, je t’ai été abandonné; depuis le sein de ma mère, c’est toi qui es mon Dieu.
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
Ne t’éloigne pas de moi, car l’angoisse est proche, car personne ne vient à mon secours.
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
Autour de moi sont de nombreux taureaux, les forts de Basan m’environnent.
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
Ils ouvrent contre moi leur gueule, comme un lion qui déchire et rugit.
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
Je suis comme de l’eau qui s’écoule, et tous mes os sont disjoints; mon cœur est comme de la cire, il se fond dans mes entrailles.
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
Ma force s’est desséchée comme un tesson d’argile, et ma langue s’attache à mon palais; tu me couches dans la poussière de la mort.
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
Car des chiens m’environnent, une troupe de scélérats rôdent autour de moi; ils ont percé mes pieds et mes mains,
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
je pourrais compter tous mes os. Eux, ils m’observent, ils me contemplent;
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
ils se partagent mes vêtements, ils tirent au sort ma tunique.
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
Et toi, Yahweh, ne t’éloigne pas! Toi qui es ma force, viens en hâte à mon secours!
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
Délivre mon âme de l’épée, ma vie du pouvoir du chien!
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
Sauve-moi de la gueule du lion, tire-moi des cornes du buffle!
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
Alors j’annoncerai ton nom à mes frères, au milieu de l’assemblée je te louerai:
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
« Vous qui craignez Yahweh, louez-le! Vous tous, postérité de Jacob, glorifiez-le! Révérez-le, vous tous, postérité d’Israël!
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
Car il n’a pas méprisé, il n’a pas rejeté la souffrance de l’affligé, il n’a pas caché sa face devant lui, et quand l’affligé a crié vers lui, il a entendu. »
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
Grâce à toi, mon hymne retentira dans la grande assemblée, j’acquitterai mes vœux en présence de ceux qui te craignent.
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
Les affligés mangeront et se rassasieront; ceux qui cherchent Yahweh le loueront. Que votre cœur revive à jamais!
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
Toutes les extrémités de la terre se souviendront et se tourneront vers Yahweh, et toutes les familles des nations se prosterneront devant sa face.
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
Car à Yahweh appartient l’empire, il domine sur les nations.
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
Les puissants de la terre mangeront et se prosterneront; devant lui s’inclineront tous ceux qui descendent à la poussière, ceux qui ne peuvent prolonger leur vie.
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
La postérité le servira; on parlera du Seigneur à la génération future.
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
Ils viendront et ils annonceront sa justice, au peuple qui naîtra, ils diront ce qu’il a fait.