< Zabura 22 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
Pour le chef musicien; réglé sur « The Dœ of the Morning ». Un psaume de David. Mon Dieu, mon Dieu, pourquoi m'as-tu abandonné? Pourquoi es-tu si loin de me secourir, et des paroles de mes gémissements?
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
Mon Dieu, je crie pendant le jour, mais tu ne réponds pas; dans la saison de la nuit, et je ne suis pas silencieux.
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
Mais toi, tu es saint, vous qui habitez les louanges d'Israël.
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
Nos pères avaient confiance en toi. Ils ont fait confiance, et vous les avez délivrés.
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
Ils ont crié vers toi, et ils ont été délivrés. Ils ont eu confiance en vous, et n'ont pas été déçus.
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
Mais moi, je suis un ver, et je ne suis pas un homme; un opprobre des hommes, et méprisé par le peuple.
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
Tous ceux qui me voient se moquent de moi. Ils m'insultent de leurs lèvres. Ils secouent la tête en disant,
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
« Il se confie en Yahvé. Laissez-le le délivrer. Qu'il le sauve, puisqu'il se complaît en lui. »
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
Mais c'est toi qui m'as fait sortir du ventre de ma mère. Tu m'as fait confiance alors que j'étais aux seins de ma mère.
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
J'ai été jeté sur toi dès le sein de ma mère. Tu es mon Dieu depuis que ma mère m'a porté.
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
Ne t'éloigne pas de moi, car le malheur est proche. Car il n'y a personne pour aider.
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
De nombreux taureaux m'ont entouré. De puissants taureaux de Bashan m'ont encerclé.
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
Ils ouvrent largement la bouche contre moi, des lions déchirant leur proie et rugissant.
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
Je suis répandu comme de l'eau. Tous mes os sont déréglés. Mon cœur est comme de la cire. Il est fondu en moi.
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
Ma force est desséchée comme un pot de fleurs. Ma langue se colle au palais. Tu m'as amené dans la poussière de la mort.
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
Car les chiens m'ont entouré. Une troupe de malfaiteurs m'a enfermé. Ils ont percé mes mains et mes pieds.
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
Je peux compter tous mes os. Ils me regardent et me fixent.
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
Ils partagent mes vêtements entre eux. Ils ont tiré au sort mes vêtements.
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
Mais ne t'éloigne pas, Yahvé. Vous êtes mon aide. Dépêchez-vous de m'aider!
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
Délivre mon âme de l'épée, ma précieuse vie du pouvoir du chien.
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
Sauve-moi de la gueule du lion! Oui, tu m'as sauvé des cornes des bœufs sauvages.
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
Je proclamerai ton nom à mes frères. Au milieu de l'assemblée, je te louerai.
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
Vous qui craignez Yahvé, louez-le! Vous tous, descendants de Jacob, glorifiez-le! Restez en admiration devant lui, vous tous, descendants d'Israël!
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
Car il n'a pas méprisé ni abhorré l'affliction des affligés, Il ne lui a pas non plus caché son visage; mais quand il a crié vers lui, il a entendu.
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
Je te loue dans la grande assemblée. J'accomplirai mes vœux devant ceux qui le craignent.
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
Les humbles mangeront et seront rassasiés. Ceux qui le cherchent loueront Yahvé. Que vos cœurs vivent à jamais.
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
Toutes les extrémités de la terre se souviendront et se tourneront vers Yahvé. Tous les parents des nations se prosterneront devant toi.
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
Car le royaume appartient à Yahvé. Il est le chef des nations.
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
Tous les riches de la terre mangeront et se prosterneront. Tous ceux qui descendent dans la poussière s'inclineront devant lui, même celui qui ne peut pas garder son âme en vie.
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
La postérité le servira. On parlera du Seigneur aux générations futures.
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
Ils viendront et annonceront sa justice à un peuple qui naîtra, car il l'a fait.

< Zabura 22 >