< Zabura 22 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
My God, my God, why have you abandoned/deserted me? Why do you stay so far from me, and why do you not hear/help me [RHQ]? Why do you not hear me when I am groaning?
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
My God, every day I call to you during the daytime and during the night, but you do not answer me, so I am not able to sleep.
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
But you are holy. You sit on your throne as king, and [we the people of] Israel praise you [PRS].
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
Our ancestors trusted in you. [Because] they trusted in you, you rescued them.
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
When they cried out to you, you saved them. They trusted in you, and (they were not disappointed/you [saved them] as you said that you would).
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
But [you have not rescued me] [People despise me and consider that I am not a man]; [they think that] I am [as worthless as] a worm! Everyone [HYP] scorns me and despises me.
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
Everyone who sees me [HYP] makes fun of me. They sneer at me and [insult me by] shaking their heads [at me as though I were an evil man]. They say,
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
“He trusts in Yahweh, so Yahweh should save him! [He says that] Yahweh is very pleased with him; if that is so, Yahweh should rescue him!”
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
[Why do] you [not] protect me [now as you did] when I was born? I was safe even when I was (nursing/drinking milk from my mother’s breasts).
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
[It was as though] you adopted me right when I was born. You have (been my God/taken care of me) ever since I was born.
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
So, (do not stay far from/stay close to) [LIT] me now because [enemies who will cause me much] trouble are near me, and there is no one [else] who can help me.
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
[My enemies] surround me [like] a herd/group of wild bulls. [Fierce people, like those] strong bulls that graze [on the hills] in Bashan [area], encircle me.
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
[They are like] roaring lions that are attacking the animals that they want to kill [MET] [and eat]; they rush toward me [to kill] me; they [are like lions that] have their mouths open, [ready to tear their victims to pieces] [MET].
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
I am completely exhausted [MET], and all my bones are out of their joints/places. I [no longer expect that God will save me]; [that expectation is gone completely], like wax that has melted away.
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
My strength is [all dried up] [MET] like a broken piece of a clay jar that has dried [in the sun]. [I am so thirsty that] my tongue sticks to the roof of my mouth. O God, [I think that you are about to let] me die and become dirt!
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
My enemies [MET] surround me like a pack/group of wild dogs. A group of evil men has encircled me, [ready to attack me]. They have [already] smashed my hands and my feet.
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
[I am so weak and thin that] my bones can be seen and counted. My enemies stare at me and (gloat/are happy) about [what has happened to] me.
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
They looked at the clothes that I [was wearing] and gambled to determine which piece each of them would get.
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
O Yahweh, do not stay far away from me! You who are my [source of] strength, come quickly and help me!
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
Rescue me from [those who want to kill me with] their swords. Save me from those who are [like wild/fierce] dogs [MET].
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
Snatch me away from [my enemies who are] like lions whose jaws [are already open, ready to chew me up] Grab me away from [those men who are like] wild oxen [that attack other animals with] their horns [MET]!
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
[But you have saved me, so] I will declare to my fellow [Israelis] how great you [MTY] are. I will praise you among the group of your people gathered [to worship you].
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
You people who have an awesome respect for Yahweh, praise him! All you who are descended from Jacob, honor Yahweh! All you Israeli people, revere him!
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
He does not despise or ignore those who are suffering; he does not hide (his face/himself) from them. He has listened to them when they cried out to him for help.
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
Yahweh, in the great gathering [of your people], I will praise you for what you have done. In the presence of those who revere you, I will offer [the sacrifices] that I promised.
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
The poor people [whom I have invited to the meal] will eat as much as they want. All who come worship Yahweh will praise him. I pray that [God will enable] you all to live a long and happy life!
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
I pray that [people in all nations, even] in the remote areas, will think about Yahweh and turn to him, and that people from all the clans in the world will bow down before him.
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
Because Yahweh is the king! He rules all the nations.
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
I desire that all the rich people on the earth will bow before him. Some day they will die, but I want them to prostrate themselves on the ground in his presence [before they die].
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
People (in the future generations/who have not been born yet) will also serve Yahweh. Our descendants will be told about what Yahweh [has done].
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
People who are not yet born, [who will live in future years], will be told how Yahweh rescued his people. People will tell them, “Yahweh did it!”

< Zabura 22 >