< Zabura 22 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
To the choirmaster on [the] doe of the dawn a psalm of David. O God my God my why? have you forsaken me [are] far from deliverance my [the] words of cry of distress my.
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
O God my I call out by day and not you answer and night and not repose [belongs] to me.
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
And you [are] holy sitting [the] praises of Israel.
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
In you they trusted ancestors our they trusted and you delivered them.
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
To you they cried out and they were delivered in you they trusted and not they were ashamed.
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
And I [am] a worm and not a man a reproach of humankind and despised of a people.
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
All [those who] see me they mock me they make a separation with a lip they shake a head.
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
Roll to Yahweh let him rescue him let him deliver him for he delights in him.
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
For you [were] drawing forth me from [the] belly [were] making trust me on [the] breasts of mother my.
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
On you I was cast from [the] womb from [the] belly of mother my [have been] God my you.
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
May not you be far from me for trouble [is] near for there not [is] a helper.
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
They have surrounded me bulls many mighty [bulls] of Bashan they have encircled me.
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
They have opened on me mouth their a lion tearing and roaring.
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
Like water I have been poured out and they have become dislocated all bones my it has become heart my like wax it has melted in [the] midst of inward parts my.
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
It has dried up like earthenware - strength my and tongue my [has been] made to cling to jaws my and to [the] dust of death you put me.
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
For they have surrounded me dogs a company of evil-doers they have encircled me (like a lion *L(D)*) hands my and feet my.
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
I count all bones my they they look they look on me.
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
They distribute clothes my to themselves and on clothing my they cast a lot.
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
And you O Yahweh may not you be distant O strength my to help my make haste!
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
Deliver! from [the] sword life my from [the] hand of a dog only [life] my.
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
Save me from [the] mouth of a lion and from [the] horns of wild oxen you have answered me.
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
I will recount name your to brothers my in among [the] assembly I will praise you.
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
O [those] fearing Yahweh - praise him O all [the] offspring of Jacob honor him and be afraid from him O all [the] offspring of Israel.
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
For not he has despised and not he has detested [the] affliction of an afflicted [person] and not he has hidden face his from him and when cried for help he to him he heard.
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
[is] from With you praise my in [the] assembly great vows my I will pay before [those] fearing him.
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
They will eat humble [people] - so they may be satisfied they will praise Yahweh [those who] seek him may it live heart your for ever.
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
They will remember - and they may turn to Yahweh all [the] ends of [the] earth so they may bow down before you all [the] clans of [the] nations.
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
For [belongs] to Yahweh the kingship and [he is] ruling over the nations.
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
They have eaten and they have bowed down - all [the] fat [people] of [the] earth before him they will bow down all [those who are] about to go down of dust and life his not he has preserved alive.
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
Offspring it will serve him it will be recounted of [the] Lord to the generation.
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
They will come and they may declare righteousness his to a people about to be born that he has acted.

< Zabura 22 >