< Zabura 22 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
For the Leader; upon Aijeleth ha-Shahar. A Psalm of David. My God, my God, why hast Thou forsaken me, and art far from my help at the words of my cry?
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
O my God, I call by day, but Thou answerest not; and at night, and there is no surcease for me.
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
Yet Thou art holy, O Thou that art enthroned upon the praises of Israel.
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
In Thee did our fathers trust; they trusted, and Thou didst deliver them.
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
Unto Thee they cried, and escaped; in Thee did they trust, and were not ashamed.
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
But I am a worm, and no man; a reproach of men, and despised of the people.
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
All they that see me laugh me to scorn; they shoot out the lip, they shake the head:
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
'Let him commit himself unto the LORD! let Him rescue him; let Him deliver him, seeing He delighteth in him.'
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
For Thou art He that took me out of the womb; Thou madest me trust when I was upon my mother's breasts.
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
Upon Thee I have been cast from my birth; Thou art my God from my mother's womb.
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
Be not far from me; for trouble is near; for there is none to help.
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
Many bulls have encompassed me; strong bulls of Bashan have beset me round.
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
They open wide their mouth against me, as a ravening and a roaring lion.
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
I am poured out like water, and all my bones are out of joint; my heart is become like wax; it is melted in mine inmost parts.
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
My strength is dried up like a potsherd; and my tongue cleaveth to my throat; and Thou layest me in the dust of death.
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
For dogs have encompassed me; a company of evil-doers have inclosed me; like a lion, they are at my hands and my feet.
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
I may count all my bones; they look and gloat over me.
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
They part my garments among them, and for my vesture do they cast lots.
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
But Thou, O LORD, be not far off; O Thou my strength, hasten to help me.
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
Deliver my soul from the sword; mine only one from the power of the dog.
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
Save me from the lion's mouth; yea, from the horns of the wild-oxen do Thou answer me.
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
I will declare Thy name unto my brethren; in the midst of the congregation will I praise Thee.
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
'Ye that fear the LORD, praise Him; all ye the seed of Jacob, glorify Him; and stand in awe of Him, all ye the seed of Israel.
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
For He hath not despised nor abhorred the lowliness of the poor; neither hath He hid His face from him; but when he cried unto Him, He heard.'
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
From Thee cometh my praise in the great congregation; I will pay my vows before them that fear Him.
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
Let the humble eat and be satisfied; let them praise the LORD that seek after Him; may your heart be quickened for ever!
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
All the ends of the earth shall remember and turn unto the LORD; and all the kindreds of the nations shall worship before Thee.
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
For the kingdom is the LORD'S; and He is the ruler over the nations.
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
All the fat ones of the earth shall eat and worship; all they that go down to the dust shall kneel before Him, even he that cannot keep his soul alive.
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
A seed shall serve him; it shall be told of the Lord unto the next generation.
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
They shall come and shall declare His righteousness unto a people that shall be born, that He hath done it.

< Zabura 22 >