< Zabura 22 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
For the music director. To the tune “Doe of the Dawn.” A psalm of David. My God, my God, why have you abandoned me? Why are you so far away when I groan, asking for help?
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
My God, every day I cry out to you, but you don't answer; at night too, but I get no rest.
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
Yet you are holy, and the praises of Israel are your throne.
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
Our forefathers trusted in you; they trusted and you rescued them.
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
They cried out to you for help, and they were saved. They trusted in you and were not defeated.
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
But I'm a worm, not a man, scorned and despised by everyone.
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
People who see me mock me. They laugh at me and shake their heads, saying,
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
“He trusts in the Lord—well then, let the Lord save him! If the Lord is such a friend, then let the Lord rescue him!”
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
However, you brought me safely through birth, and led me to trust in you at my mother's breasts.
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
I was entrusted to you from birth; from the time I was born you have been my God.
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
Do not be distant from me, because trouble is close by and no one else can help.
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
Enemies surround me like a herd of bulls; strong bulls from Bashan have encircled me.
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
Like roaring lions tearing at their prey they open their mouths wide against me.
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
I feel like I'm being poured out like water. I'm falling apart as if all my bones have become loose. My mind feels like it's wax melting inside me.
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
My strength has dried up like a piece of broken pottery. My tongue is stuck to the roof of my mouth. You're burying me as if I'm already dead.
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
Evil men surround me like a pack of dogs. They have pierced my hands and feet.
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
I'm so thin I can count all my bones. People stare at me and gloat.
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
They divide my clothing among them; they roll dice for my clothes.
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
But you, Lord, don't be far away from me! You are my strength—hurry, come and help me!
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
Save me from death by the sword! Save my life—the only one I have—from the dogs!
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
Rescue me from the mouth of the lion and from the wild bulls!
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
I will tell my people all the wonderful things you have done; I will praise you in the congregation.
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
Praise the Lord, all who worship him! Honor him, every descendant of Jacob! Be in awe of him, every descendant of Israel!
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
For he has not ridiculed or scorned the suffering of the poor; he has not turned away from them, he has listened to their cries for help.
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
You are the subject of my praise in the great assembly. I will fulfill my promises before those who worship you.
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
The poor shall eat, and they shall be satisfied. All who come to the Lord will praise him—may you all live forever!
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
Everyone in the whole world will repent and return to the Lord; all the nations will worship before you.
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
For kingly power belongs to the Lord; he is the one who rules over the nations.
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
All who prosper come to feast and worship. Bow down before him, all those destined for the grave—for none can keep themselves alive.
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
Our descendants will serve him; they will tell the next generation about the Lord.
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
They will come and tell those yet to be born how good the Lord is, and all that he has done!