< Zabura 22 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
(Til sangmesteren. Efter "morgenrødens hind". En salme af David.) Min Gud, min Gud, hvorfor har du forladt mig? Mit Skrig til Trods er Frelsen mig fjern.
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
Min Gud, jeg råber om Dagen, du svarer ikke, om Natten, men finder ej Hvile.
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
Og dog er du den hellige, som troner på Israels Lovsange.
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
På dig forlod vore Fædre sig, forlod sig, og du friede dem;
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
de råbte til dig og frelstes, forlod sig på dig og blev ikke til Skamme.
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
Men jeg er en Orm og ikke en Mand, til Spot for Mennesker, Folk til Spe;
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
alle, der ser mig, håner mig, vrænger Mund og ryster på Hovedet:
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
"Han har væltet sin Sag på HERREN; han fri ham og frelse ham, han har jo Velbehag i ham."
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
Ja, du drog mig af Moders Liv, lod mig hvile trygt ved min Moders Bryst;
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
på dig blev jeg kastet fra Moders Skød, fra Moders Liv var du min Gud.
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
Vær mig ikke fjern, thi Trængslen er nær, og ingen er der, som hjælper!
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
Stærke Tyre står omkring mig, Basans vældige omringer mig,
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
spiler Gabet op imod mig som rovgridske, brølende Løver.
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
Jeg er som Vand, der er udgydt, alle mine Knogler skilles, mit Hjerte er blevet som Voks, det smelter i Livet på mig;
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
min Gane er tør som et Potteskår til Gummerne klæber min Tunge, du lægger mig ned i Dødens Støv.
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
Thi Hunde står omkring mig, onde i Flok omringer mig, de har gennemboret mine Hænder og Fødder,
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
jeg kan tælle alle mine Ben; med Skadefryd ser de på mig.
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
Mine Klæder deler de mellem sig, om Kjortelen kaster de Lod.
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
Men du, o HERRE, vær ikke fjern, min Redning, il mig til Hjælp!
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
Udfri min Sjæl fra Sværdet, min eneste af Hundes Vold!
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
Frels mig fra Løvens Gab, fra Vildoksens Horn! Du har bønhørt mig.
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
Dit Navn vil jeg kundgøre for mine Brødre, prise dig midt i Forsamlingen:
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
"I, som frygter HERREN, pris ham, ær ham; al Jakobs Æt, bæv for ham, al Israels Æt!
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
Thi han foragtede ikke, forsmåede ikke den armes Råb, skjulte ikke sit Åsyn for ham, men hørte, da han råbte til ham!"
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
Jeg vil synge din Pris i en stor Forsamling, indfri mine Løfter iblandt de fromme;
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
de ydmyge skal spise og mættes; hvo HERREN søger, skal prise ham; deres Hjerte leve for evigt!
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
Den vide Jord skal mærke sig det og omvende sig til HERREN, og alle Folkenes Slægter skal tilbede for hans Åsyn;
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
thi HERRENs er Riget, han er Folkenes Hersker.
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
De skal tilbede ham alene, alle Jordens mægtige; de skal bøje sig for hans Åsyn, alle, der nedsteg i Støvet og ikke holdt deres Sjæl i Live.
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
Ham skal Efterkommeme tjene; om HERREN skal tales til Slægten, der kommer;
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
de skal forkynde et Folk, der fødes, hans Retfærd. Thi han greb ind.

< Zabura 22 >