< Zabura 22 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
Til Sangmesteren; til “Morgenrødens Hind”; en Psalme af David.
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
Min Gud, min Gud! hvorfor har du forladt mig, du er fjern fra min Frelse, fra mit Klageskrig.
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
Min Gud! jeg raaber om Dagen, og du svarer ikke; og om Natten, og jeg kan ikke være stille.
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
Men du er hellig, du, som bor iblandt Israels Lovsange!
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
Vore Fædre forlode sig paa dig; de forlode sig paa dig, og du friede dem.
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
Til dig raabte de og frelstes; de forlode sig paa dig, og bleve ikke beskæmmede.
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
Men jeg er en Orm og ikke en Mand, Menneskens Spot og Folks Foragt.
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
Alle de, som se mig, spotte mig; de vrænge Mund, de ryste med Hovedet:
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
“Vælt det paa Herren, han befri ham; han redde ham, efterdi han har Lyst til ham”!
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
Du er dog den, som drog mig af Moders Liv, du lod mig hvile trygt ved min Moders Bryster.
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
Paa dig er jeg kastet fra Moders Liv af; du er min Gud fra min Moders Skød.
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
Vær ikke langt fra mig, thi Angest er nær; thi der er ingen Hjælper.
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
Mange Øksne have omgivet mig; Basans Tyre have omringet mig.
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
De oplode deres Gab imod mig som en Løve, der river og brøler.
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
Jeg er udøst som Vand, og alle mine Ben adskille sig; mit Hjerte er som Voks, det smelter midt i mit Liv.
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
Min Kraft er tørret som et Potteskaar, min Tunge hænger ved mine Gummer, og du lægger mig ned i Dødens Støv.
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
Thi Hunde have omgivet mig; de ondes Hob har omringet mig; de have gennemboret mine Hænder og mine Fødder.
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
Jeg kan tælle alle mine Ben; de se til, de se paa mig.
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
De dele mine Klæder imellem sig og kaste Lod om mit Klædebon.
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
Men du, Herre, vær ikke langt borte! min Styrke, skynd dig at hjælpe mig!
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
Red min Sjæl fra Sværdet, min eneste fra Hundes Vold!
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
Frels mig fra Løvens Gab og fra Enhjørningens Horn! Du har bønhørt mig.
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
Jeg vil forkynde dit Navn for mine Brødre, midt i Forsamlingen vil jeg love dig.
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
I, som frygte Herren, lover ham! al Jakobs Sæd, ærer ham! og bæver for ham, al Israels Sæd!
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
Thi han har ikke foragtet og ej havt Vederstyggelighed for den elendiges Elendighed og ikke skjult sit Ansigt for ham; men der han raabte til ham, hørte han det.
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
Fra dig begynder min Lovsang i en stor Forsamling; jeg vil betale mine Løfter i Paasyn af dem, som frygte ham.
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
De sagtmodige skulle æde og mættes, Herren skal prises af dem, som søge ham; eders Hjerter leve altid!
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
Alle Verdens Ender skulle komme det i Hu og omvende sig til Herren; og alle Hedningernes Slægter skulle tilbede for dit Ansigt.
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
Thi Riget hører Herren til, og han hersker over Hedningerne.
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
Alle mægtige paa Jorden skulle æde og tilbede; for ham skulle alle de bøje sig, som sank i Muld, og den, som ikke kunde holde sin Sjæl i Live.
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
Efterkommerne skulle tjene ham; der skal fortælles om Herren til Efterslægten. De skulle komme og forkynde hans Retfærdighed for det Folk, som bliver født; thi han har gjort det.