< Zabura 22 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
大衛的詩,交與伶長。調用朝鹿。 我的上帝,我的上帝!為甚麼離棄我? 為甚麼遠離不救我?不聽我唉哼的言語?
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
我的上帝啊,我白日呼求,你不應允, 夜間呼求,並不住聲。
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
但你是聖潔的, 是用以色列的讚美為寶座的。
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
我們的祖宗倚靠你; 他們倚靠你,你便解救他們。
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
他們哀求你,便蒙解救; 他們倚靠你,就不羞愧。
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
但我是蟲,不是人, 被眾人羞辱,被百姓藐視。
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
凡看見我的都嗤笑我; 他們撇嘴搖頭,說:
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
他把自己交託耶和華,耶和華可以救他吧! 耶和華既喜悅他,可以搭救他吧!
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
但你是叫我出母腹的; 我在母懷裏,你就使我有倚靠的心。
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
我自出母胎就被交在你手裏; 從我母親生我,你就是我的上帝。
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
求你不要遠離我! 因為急難臨近了,沒有人幫助我。
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
有許多公牛圍繞我, 巴珊大力的公牛四面困住我。
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
牠們向我張口, 好像抓撕吼叫的獅子。
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
我如水被倒出來; 我的骨頭都脫了節; 我心在我裏面如蠟鎔化。
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
我的精力枯乾,如同瓦片; 我的舌頭貼在我牙床上。 你將我安置在死地的塵土中。
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
犬類圍着我,惡黨環繞我; 他們扎了我的手,我的腳。
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
我的骨頭,我都能數過; 他們瞪着眼看我。
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
他們分我的外衣, 為我的裏衣拈鬮。
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
耶和華啊,求你不要遠離我! 我的救主啊,求你快來幫助我!
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
求你救我的靈魂脫離刀劍, 救我的生命脫離犬類,
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
救我脫離獅子的口; 你已經應允我,使我脫離野牛的角。
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
我要將你的名傳與我的弟兄, 在會中我要讚美你。
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
你們敬畏耶和華的人要讚美他! 雅各的後裔都要榮耀他! 以色列的後裔都要懼怕他!
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
因為他沒有藐視憎惡受苦的人, 也沒有向他掩面; 那受苦之人呼籲的時候,他就垂聽。
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
我在大會中讚美你的話是從你而來的; 我要在敬畏耶和華的人面前還我的願。
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
謙卑的人必吃得飽足; 尋求耶和華的人必讚美他。 願你們的心永遠活着!
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
地的四極都要想念耶和華,並且歸順他; 列國的萬族都要在你面前敬拜。
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
因為國權是耶和華的; 他是管理萬國的。
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
地上一切豐肥的人必吃喝而敬拜; 凡下到塵土中-不能存活自己性命的人 -都要在他面前下拜。
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
他必有後裔事奉他; 主所行的事必傳與後代。
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
他們必來把他的公義傳給將要生的民, 言明這事是他所行的。

< Zabura 22 >