< Zabura 21 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
För sångmästaren; en psalm av David. HERRE, över din makt gläder sig konungen; huru fröjdas han icke högeligen över din seger!
2 Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
Vad hans hjärta önskar har du givit honom, och hans läppars begäran har du icke vägrat honom. (Sela)
3 Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
Ty du kommer honom till mötes med välsignelser av vad gott är; du sätter på hans huvud en gyllene krona.
4 Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
Han bad dig om liv, och du gav honom det, ett långt liv alltid och evinnerligen.
5 Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
Stor är hans ära genom din seger; majestät och härlighet beskär du honom.
6 Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
Ja, du låter honom bliva till välsignelse evinnerligen; du fröjdar honom med glädje inför ditt ansikte.
7 Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
Ty konungen förtröstar på HERREN, och genom den Högstes nåd skall han icke vackla.
8 Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
Din hand skall nå alla dina fiender; din högra hand skall träffa dem som hata dig.
9 A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
Du skall låta dem känna det såsom i en glödande ugn, när du låter se ditt ansikte. HERREN skall fördärva dem i sin vrede; eld skall förtära dem.
10 Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
Deras livsfrukt skall du utrota från jorden och deras avkomma från människors barn.
11 Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
Ty de ville draga ont över dig; de tänkte ut ränker, men de förmå intet.
12 gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
Nej, du skall driva dem tillbaka; med din båge skall du sikta mot deras anleten.
13 Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.
Upphöjd vare du, HERREN, i din makt; vi vilja besjunga och lovsäga din hjältekraft.