< Zabura 21 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
Jehová, en tu fortaleza se alegrará el rey; y en tu salud se regocijará mucho.
2 Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
El deseo de su corazón le diste; y no le negaste lo que sus labios pronunciaron. (Selah)
3 Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
Por tanto le adelantarás en bendiciones de bien: corona de oro fino has puesto sobre su cabeza.
4 Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
Vida te demandó, se la diste: longura de días, por siglo y siglo.
5 Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
Grande es su gloria en tu salud: honra y hermosura has puesto sobre él.
6 Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
Porque le has bendecido para siempre: alegrástele de alegría con tu rostro.
7 Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
Por cuanto el rey confía en Jehová: y en la misericordia del Altísimo no titubeará.
8 Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
Alcanzará tu mano a todos tus enemigos: tu diestra alcanzará a los que te aborrecen.
9 A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
Ponerlos has como horno de fuego en el tiempo de tu ira: Jehová los deshará en su furor, y fuego los consumirá.
10 Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
Su fruto destruirás de la tierra: y su simiente de entre los hijos de los hombres.
11 Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
Porque tendieron mal contra ti: maquinaron maquinación, mas no prevalecieron.
12 gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
Por tanto ponerlos has a parte: con tus cuerdas apuntarás a sus rostros.
13 Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.
Ensálzate, o! Jehová, con tu fortaleza: cantaremos y alabaremos tu valentía.

< Zabura 21 >