< Zabura 21 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
Oh Yavé, el rey se alegrará en tu poder, Y en tu salvación ¡cuánto se regocijará!
2 Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
Le diste el deseo de su corazón Y no le retuviste la petición de sus labios. (Selah)
3 Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
Con bendiciones de bien saliste a su encuentro. Corona de oro puro pusiste en su cabeza.
4 Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
Vida te pidió, Y se la concediste, Largura de días, eternamente y para siempre.
5 Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
Grande es su gloria por tu salvación. Pusiste sobre él honor y majestad.
6 Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
Lo bendijiste para siempre. Lo llenaste de alegría con tu Presencia
7 Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
Por cuanto el rey confía en Yavé. Por la misericordia de ʼElyón, no será conmovido.
8 Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
Tu mano alcanzará a todos tus enemigos. Tu mano derecha alcanzará a los que te aborrecen.
9 A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
Los pondrás en horno de fuego en el tiempo de tu ira. Yavé los deshará en su ira, Y el fuego los consumirá.
10 Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
Destruirás su producto de la tierra, Y su descendencia de entre los hijos de hombres.
11 Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
Porque tramaron el mal contra Ti. Fraguaron un complot, Pero no prevalecerán.
12 gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
Pues Tú les harás volver la espalda Al apuntar tu arco contra sus rostros.
13 Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.
¡Engrandécete, oh Yavé, con tu fortaleza! Cantaremos y alabaremos tu poderío.

< Zabura 21 >