< Zabura 21 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
O rei se alegra em tua força, Senhor; e na tua salvação grandemente se regozija.
2 Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
Cumpriste-lhe o desejo do seu coração, e não negaste as suplicas dos seus lábios (Selah)
3 Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
Pois o prevines das bençãos de bondade; pões na sua cabeça uma coroa de ouro fino
4 Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
Vida te pediu, e lha deste, mesmo longura de dias para sempre e eternamente.
5 Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
Grande é a sua glória pela tua salvação; glória e magestade puseste sobre ele.
6 Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
Pois o abençoaste para sempre: tu o enches de gozo com a tua face.
7 Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
Porque o rei confia no Senhor, e pela misericórdia do altíssimo nunca vacilará.
8 Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
A tua mão alcançará todos os teus inimigos, a tua mão direita alcançará aqueles que te aborrecem.
9 A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
Tu os farás como um forno de fogo no tempo da tua ira; o Senhor os devorará na sua indignação, e o fogo os consumirá.
10 Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
Seu fruto destruirás da terra, e a sua semente dentre os filhos dos homens.
11 Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
Porque intentaram o mal contra ti; maquinaram uma trapaça, mas não prevalecerão.
12 gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
Portanto tu lhes farás voltar as costas; e com tuas flechas postas nas cordas lhes apontarás ao rosto.
13 Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.
Exalta-te, Senhor, na tua força; então cantaremos e louvaremos o teu poder.

< Zabura 21 >