< Zabura 21 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
O rei se alegra em tua força, Senhor; e na tua salvação grandemente se regozija.
2 Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
Cumpriste-lhe o desejo do seu coração, e não negaste as supplicas dos seus labios (Selah)
3 Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
Pois o prevines das bençãos de bondade; pões na sua cabeça uma corôa d'oiro fino
4 Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
Vida te pediu, e lh'a déste, mesmo longura de dias para sempre e eternamente.
5 Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
Grande é a sua gloria pela tua salvação; gloria e magestade pozeste sobre elle.
6 Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
Pois o abençoaste para sempre: tu o enches de gozo com a tua face.
7 Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
Porque o rei confia no Senhor, e pela misericordia do Altissimo nunca vacillará.
8 Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
A tua mão alcançará todos os teus inimigos, a tua mão direita alcançará aquelles que te aborrecem.
9 A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
Tu os farás como um forno de fogo no tempo da tua ira; o Senhor os devorará na sua indignação, e o fogo os consumirá.
10 Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
Seu fructo destruirás da terra, e a sua semente d'entre os filhos dos homens.
11 Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
Porque intentaram o mal contra ti; machinaram uma trapaça, mas não prevalecerão.
12 gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
Portanto tu lhes farás voltar as costas; e com tuas frechas postas nas cordas lhes apontarás ao rosto.
13 Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.
Exalta-te, Senhor, na tua força; então cantaremos e louvaremos o teu poder.

< Zabura 21 >