< Zabura 21 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
Jehova, inkosi izajabula emandleni akho, lesindisweni lwakho izathaba kangakanani!
2 Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
Uyinikile isifiso senhliziyo yayo, kawuyincitshanga isicelo sendebe zayo. (Sela)
3 Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
Ngoba uyihlangabeze ngezibusiso zokuhle, wayethwesa umqhele wegolide elihle ekhanda layo.
4 Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
Yacela impilo kuwe, wayinika yona, ubude bezinsuku kuze kube nini lanini.
5 Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
Lukhulu udumo lwayo ekusindiseni kwakho, inkazimulo lobukhosi wakubeka phezu kwayo.
6 Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
Ngoba uyenze yabusiseka kakhulu kuze kube nininini, uyayithokozisa ngenjabulo ebukhoneni bakho.
7 Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
Ngoba inkosi ithembela kuJehova, langomusa woPhezukonke kayiyikunyikinywa.
8 Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
Isandla sakho sizazithola zonke izitha zakho, lesandla sakho sokunene sizabathola labo abakuzondayo.
9 A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
Uzabenza babe njengesithando somlilo esikhathini solaka lwakho. INkosi izabaginya ekuthukutheleni kwayo, lomlilo uzabaqothula.
10 Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
Uzachitha isithelo sabo emhlabeni, lenzalo yabo phakathi kwabantwana babantu.
11 Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
Ngoba bezimisela okubi bemelene lawe, beceba ugobe, bazakwehluleka.
12 gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
Ngoba uzabafulathelisa, ngezintambo zedandili uzalungisa imitshoko imelane lobuso babo.
13 Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.
Phakama, Nkosi, ngamandla akho! Sizahlabela sidumise amandla akho.

< Zabura 21 >