< Zabura 21 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
Per il Capo de’ musici. Salmo di Davide. O Eterno, il re si rallegra nella tua forza; ed oh quanto esulta per la tua salvezza!
2 Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
Tu gli hai dato il desiderio del suo cuore e non gli hai rifiutata la richiesta delle sue labbra. (Sela)
3 Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
Poiché tu gli sei venuto incontro con benedizioni eccellenti, gli hai posta in capo una corona d’oro finissimo.
4 Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
Egli t’avea chiesto vita, e tu gliel’hai data: lunghezza di giorni perpetua ed eterna.
5 Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
Grande è la sua gloria mercé la tua salvezza. Tu lo rivesti di maestà e di magnificenza;
6 Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
poiché lo ricolmi delle tue benedizioni in perpetuo, lo riempi di gioia nella tua presenza.
7 Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
Perché il re si confida nell’Eterno, e, per la benignità dell’Altissimo, non sarà smosso.
8 Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
La tua mano troverà tutti i tuoi nemici; la tua destra raggiungerà quelli che t’odiano.
9 A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
Tu li metterai come in una fornace ardente, quando apparirai; l’Eterno, nel suo cruccio, li inabisserà, e il fuoco li divorerà.
10 Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
Tu farai sparire il loro frutto dalla terra e la loro progenie di tra i figli degli uomini;
11 Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
perché hanno ordito del male contro a te; han formato malvagi disegni, che non potranno attuare;
12 gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
poiché tu farai loro voltar le spalle, col tuo arco mirerai diritto alla loro faccia.
13 Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.
Innalzati, o Eterno, con la tua forza; noi canteremo e celebreremo la tua potenza.