< Zabura 21 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
Untuk pemimpin kor. Mazmur Daud. Ya TUHAN, raja bergembira karena Engkau telah menguatkan dia; ia bersukacita karena kemenangan yang Kauberi kepadanya!
2 Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
Engkau telah memenuhi keinginan hatinya, dan memberi apa yang dimintanya.
3 Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
Engkau datang kepadanya dengan berkat berlimpah, dan memasang mahkota emas di atas kepalanya.
4 Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
Ia mohon hidup, dan Kauberikan kepadanya, bahkan umur panjang untuk selama-lamanya.
5 Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
Karena pertolongan-Mu ia menjadi sangat terhormat, Kaujadikan dia masyhur dan bersemarak.
6 Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
Kauberkati dia untuk seterusnya; kehadiran-Mu membuat ia penuh sukacita.
7 Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
Raja berharap kepada TUHAN Yang Mahatinggi, ia selalu aman sebab tetap dikasihi TUHAN.
8 Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
Ia akan menawan semua musuhnya, dan menangkap semua orang yang membenci Dia.
9 A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
Ia datang seperti api yang menyala-nyala untuk membinasakan mereka. Mereka akan dimusnahkan oleh kemarahan TUHAN, dan oleh api yang menghanguskan.
10 Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
Dari keturunan mereka tak ada yang tersisa, raja akan menumpas mereka semua.
11 Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
Apabila mereka membuat rencana menentang raja, tipu muslihat mereka tak akan berhasil.
12 gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
Ia akan membidikkan panah-Nya, sehingga mereka berbalik dan lari.
13 Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.
Kami memuji Engkau TUHAN, sebab besarlah kuasa-Mu, kami menyanyi memuji keperkasaan-Mu.