< Zabura 21 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
Dem Musikmeister. Ein Psalm Davids. Jahwe, über deine Macht freut sich der König und über deine Hilfe - wie frohlockt er so sehr!
2 Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
Du gabst ihm, was sein Herz begehrte, und was seine Lippen wünschten, verweigertest du nicht. (Sela)
3 Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
Denn du kamst ihm entgegen mit Segnungen an Glück, setztest auf sein Haupt eine Krone von Feingold.
4 Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
Leben erbat er von dir, du gabst es ihm - langes Leben für immer und ewig.
5 Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
Groß ist sein Ruhm durch deine Hilfe, Majestät und Hoheit legtest du auf ihn.
6 Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
Denn du setzest ihn zu großem Segen für immer, erfreust ihn mit Wonne vor deinem Angesicht.
7 Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
Denn der König vertraut auf Jahwe, und die Huld des Höchsten macht, daß er nicht wankt.
8 Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
Deine Hand wird alle deine Feinde erreichen, deine Rechte wird erreichen, die dich hassen.
9 A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
Du wirst sie einem Feuerofen gleich machen, wenn du erscheinst; Jahwe wird sie in seinem Zorne vertilgen und Feuer sie verzehren.
10 Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
Ihre Frucht wirst du von der Erde hinwegtilgen und ihre Nachkommen aus den Menschenkindern.
11 Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
Wenn sie Böses auf dich herabsenken wollen, Tückisches ersinnen, werden sie nichts ausrichten.
12 gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
Denn du wirst sie in die Flucht schlagen, mit deinen Sehnen auf ihre Gesichter zielen.
13 Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.
Erhebe dich, Jahwe, in deiner Macht, so wollen wir singen und preisen deine Stärke!

< Zabura 21 >