< Zabura 21 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
Auf den Siegesspender, ein Lied, von David. Ein König freut sich über Deine Macht, und wie frohlockt er über Deine Hilfe, Herr!
2 Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
Erfüllt hast Du ihm seinen Herzenswunsch, ihm nicht versagt, was seine Lippen sich erfleht. (Sela)
3 Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
Entgegen kamst Du ihm mit reichem Segen und setztest eine goldene Krone ihm aufs Haupt.
4 Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
Um Leben hat er Dich gebeten; Du hast's ihm geschenkt, ein langes Leben, unvergänglich.
5 Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
Sein Ruhm wird groß durch Deine Hilfe; Du hüllest ihn in Glanz und Majestät.
6 Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
Du machst zum Segen ihn für immerdar und labst ihn mit den Wonnen Deines Angesichtes. -
7 Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
Ja, auf den Herrn vertraut der König und zweifelt nimmer an des Höchsten Huld. -
8 Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
Gewachsen allen Deinen Feinden zeigt sich Deine Hand, gewachsen Deine Rechte allen denen, die Dich hassen.
9 A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
Zur rechten Zeit, o Herr, machst Du Dein Angesicht zur Feueresse, die sie mit ihrer Glut vernichtet, und Feuer frißt sie auf.
10 Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
Du tilgst vom Boden ihre Frucht und aus den Menschenkindern ihren Stamm,
11 Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
Weil sie mit Bösem Dir gedroht und Pläne sich ersonnen, wie sie es nimmer durften.
12 gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
Denn grausam wirfst Du diese hinund zielst mit Deinem Bogen auf ihr Angesicht.
13 Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.
Erhebe, Herr, Dich wiederum in Deiner Kraft! Wir möchten Deinen Sieg mit Sang und Spielen feiern.