< Zabura 21 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
Au chef des chantres. Psaume de David. Éternel! Le roi se réjouit de ta protection puissante. Oh! Comme ton secours le remplit d’allégresse!
2 Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
Tu lui as donné ce que désirait son cœur, Et tu n’as pas refusé ce que demandaient ses lèvres. (Pause)
3 Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
Car tu l’as prévenu par les bénédictions de ta grâce, Tu as mis sur sa tête une couronne d’or pur.
4 Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
Il te demandait la vie, tu la lui as donnée, Une vie longue pour toujours et à perpétuité.
5 Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
Sa gloire est grande à cause de ton secours; Tu places sur lui l’éclat et la magnificence.
6 Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
Tu le rends à jamais un objet de bénédictions, Tu le combles de joie devant ta face.
7 Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
Le roi se confie en l’Éternel; Et, par la bonté du Très-Haut, il ne chancelle pas.
8 Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
Ta main trouvera tous tes ennemis, Ta droite trouvera ceux qui te haïssent.
9 A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
Tu les rendras tels qu’une fournaise ardente, Le jour où tu te montreras; L’Éternel les anéantira dans sa colère, Et le feu les dévorera.
10 Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
Tu feras disparaître leur postérité de la terre, Et leur race du milieu des fils de l’homme.
11 Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
Ils ont projeté du mal contre toi, Ils ont conçu de mauvais desseins, mais ils seront impuissants.
12 gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
Car tu leur feras tourner le dos, Et avec ton arc tu tireras sur eux.
13 Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.
Lève-toi, Éternel, avec ta force! Nous voulons chanter, célébrer ta puissance.

< Zabura 21 >