< Zabura 21 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
Jusqu'à la Fin, psaume de David. Seigneur, le roi se réjouira de ta puissance; il sera, dans l'excès de sa joie, sauvé par toi.
2 Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
Tu l'as gratifié selon les désirs de son âme; tu ne l'as point sevré de ce que demandaient ses lèvres.
3 Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
Tu l'as prévenu des bénédictions de ta douceur; tu as posé sur sa tête une couronne de pierres précieuses.
4 Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
Il t'a demandé la vie, et tu lui as donné de longs jours qui s'étendront dans tous les siècles, des siècles.
5 Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
Sa gloire est grande d'avoir été sauvé par toi; tu as mis sur lui la gloire et la magnificence.
6 Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
Car tu le béniras dans tous les siècles des siècles; tu le combleras de joie en lui montrant ta face.
7 Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
Aussi le roi espère dans le Seigneur; grâce à la miséricorde du Très- Haut, il ne sera jamais ébranlé.
8 Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
Que tous tes ennemis trouvent ta main; que ta droite trouve tous ceux qui te haïssent.
9 A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
Au temps où ta face se tournera contre eux, tu les brûleras comme dans une fournaise embrasée; le Seigneur les troublera de sa colère, et le feu les dévorera.
10 Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
Tu détruiras leurs fruits sur la terre, et leurs fils d'entre les fils des hommes,
11 Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
Parce qu'ils ont voulu déverser sur toi le mal; ils ont conçu des desseins dont ils ne pourront venir à bout.
12 gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
Aussi tu leur feras tourner le dos; et pour recevoir tes derniers coups, tu retourneras leur visage.
13 Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.
Lève-toi, Seigneur, en ta force; nous célébrerons et nous chanterons tes grandeurs.

< Zabura 21 >