< Zabura 21 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
Pour le chef musicien. Un psaume de David. Le roi se réjouit de ta force, Yahvé! Comme il se réjouit de votre salut!
2 Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
Tu lui as donné le désir de son cœur, et n'ont pas retenu la demande de ses lèvres. (Selah)
3 Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
Car tu le rencontres avec les bienfaits de la bonté. Tu as mis une couronne d'or fin sur sa tête.
4 Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
Il vous a demandé la vie et vous la lui avez donnée, même durée des jours pour les siècles des siècles.
5 Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
Sa gloire est grande dans votre salut. Vous lui rendez honneur et majesté.
6 Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
Car vous le rendez très béni pour toujours. Vous le rendez heureux de joie en votre présence.
7 Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
Car le roi se confie en Yahvé. Grâce à la bonté du Très-Haut, il ne sera pas ébranlé.
8 Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
Ta main découvrira tous tes ennemis. Ta main droite découvrira ceux qui te détestent.
9 A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
Tu les rendras comme une fournaise ardente au moment de ta colère. Yahvé les engloutira dans sa colère. Le feu les dévorera.
10 Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
Tu feras disparaître leurs descendants de la terre, leur postérité d'entre les enfants des hommes.
11 Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
Car ils ont eu des intentions mauvaises à votre égard. Ils ont comploté contre vous un mal qui ne peut réussir.
12 gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
Car tu leur feras tourner le dos, quand vous pointez un arc sur leur visage.
13 Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.
Sois exalté, Yahvé, dans ta force, ainsi nous chanterons et louerons ta puissance.

< Zabura 21 >