< Zabura 21 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
“For the leader of the music. A psalm of David.” The king rejoiceth in thy strength, O LORD! Yea, he doth greatly exult in thy protection.
2 Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
Thou hast given him his heart's desire, And hast not denied him the request of his lips. (Pause)
3 Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
Yea, thou hast met him with rich blessings, Thou hast placed a crown of pure gold upon his head.
4 Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
He asked life of thee; thou gavest it him; Even long life, enduring for ever.
5 Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
Great is his glory through thine aid; Honor and majesty hast thou laid upon him.
6 Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
Thou hast made him blessed for evermore; Thou hast made him glad with the joy of thy countenance.
7 Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
For the king trusteth in the LORD; And through the goodness of the Most High he shall never fall.
8 Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
Thy hand shall overtake all thine enemies; Thy right hand shall overtake them that hate thee.
9 A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
Thou wilt make them like a burning oven in the time of thine anger; Jehovah shall swallow them up in his wrath, And the fire shall devour them.
10 Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
Their offspring shalt thou destroy from the earth, And their posterity from the sons of men.
11 Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
For they spread a net of mischief against thee; They devised plots against thee, but they did not prevail.
12 gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
Therefore thou wilt cause them to turn their backs; Thou wilt make ready thine arrows upon the strings against them.
13 Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.
Exalt thyself, O LORD! by thy strength! So will we sing, and praise thy mighty deeds.