< Zabura 2 >

1 Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
Nedir uluslar arasındaki bu kargaşa, Neden boş düzenler kurar bu halklar?
2 Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
Dünyanın kralları saf bağlıyor, Hükümdarlar birleşiyor RAB'be ve meshettiği krala karşı.
3 Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
“Koparalım onların kayışlarını” diyorlar, “Atalım üzerimizden bağlarını.”
4 Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
Göklerde oturan Rab gülüyor, Onlarla eğleniyor.
5 Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
Sonra öfkeyle uyarıyor onları, Gazabıyla dehşete düşürüyor
6 “Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
Ve, “Ben kralımı Kutsal dağım Siyon'a oturttum” diyor.
7 Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
RAB'bin bildirisini ilan edeceğim: Bana, “Sen benim oğlumsun” dedi, “Bugün ben sana baba oldum.
8 Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
Dile benden, miras olarak sana ulusları, Mülk olarak yeryüzünün dört bucağını vereyim.
9 Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
Demir çomakla kıracaksın onları, Çömlek gibi parçalayacaksın.”
10 Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
Ey krallar, akıllı olun! Ey dünya önderleri, ders alın!
11 Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
RAB'be korkuyla hizmet edin, Titreyerek sevinin.
12 Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
Oğulu öpün ki öfkelenmesin, Yoksa izlediğiniz yolda mahvolursunuz. Çünkü öfkesi bir anda alevleniverir. Ne mutlu O'na sığınanlara!

< Zabura 2 >