< Zabura 2 >

1 Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
Varför larma hedningarna och tänka folken fåfänglighet?
2 Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
Jordens konungar resa sig upp, och furstarna rådslå med varandra, mot HERREN och hans smorde:
3 Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
"Låt oss slita sönder deras bojor och kasta deras band ifrån oss."
4 Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
Han som bor i himmelen ler, HERREN bespottar dem.
5 Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
Då talar han till dem i sin vrede, och i sin förgrymmelse förskräcker han dem:
6 “Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
"Jag själv har insatt min konung på Sion, mitt heliga berg."
7 Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
Jag vill förtälja om vad beslutet är; HERREN sade till mig: "Du är min son, jag har i dag fött dig.
8 Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
Begär av mig, så skall jag giva dig hedningarna till arvedel och jordens ändar till egendom.
9 Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
Du skall sönderslå dem med järnspira, såsom lerkärl skall du krossa dem."
10 Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
Så kommen nu till förstånd, I konungar; låten varna eder, I domare på jorden.
11 Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
Tjänen HERREN med fruktan, och fröjden eder med bävan.
12 Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
Hyllen sonen, så att han icke vredgas och I förgåns på eder väg; ty snart kunde hans vrede upptändas. Saliga äro alla de som taga sin tillflykt till honom.

< Zabura 2 >