< Zabura 2 >

1 Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
¿Para qué están en tumulto las naciones, Y los pueblos maquinan cosas vanas?
2 Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
Los reyes de la tierra se levantarán, Y gobernantes conspirarán unidos Contra Yavé y contra su Ungido, y dicen:
3 Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
¡Rompamos sus ataduras Y quitemos de nosotros sus cuerdas!
4 Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
El que está sentado en los cielos se reirá. ʼAdonay se burlará de ellos.
5 Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
Luego les hablará en su furor. Los conturbará en su ira.
6 “Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
Yo mismo consagré a mi Rey sobre Sion, Mi Montaña Santa.
7 Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
Yo promulgaré el decreto. Yavé me dijo: Mi Hijo eres Tú, Yo te engendré hoy.
8 Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
Pídeme y te daré los pueblos en posesión, Y como herencia tuya los confines de la tierra.
9 Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
Los quebrantarás con vara de hierro. Los harás añicos como vasija de alfarero.
10 Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
Ahora pues, oh reyes, actúen con sabiduría. Acepten amonestación, jueces de la tierra:
11 Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
Sirvan a Yavé con temor Y regocíjense con temblor.
12 Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
Besen los pies al Hijo No sea que se enoje y perezcan en el camino, Pues de repente arde su ira. Inmensamente felices son los que se refugian en Él.

< Zabura 2 >