< Zabura 2 >

1 Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
Pourquoi se mutinent les nations, et pourquoi les peuples projettent-ils des choses vaines?
2 Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
Les Rois de la terre se trouvent en personne, et les Princes consultent ensemble contre l'Eternel, et contre son Oint.
3 Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
Rompons, [disent-ils], leurs liens, et jetons loin de nous leurs cordes.
4 Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
Celui qui habite dans les cieux se rira d'eux; le Seigneur s'en moquera.
5 Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
Alors il leur parlera en sa colère, et il les remplira de terreur par la grandeur de son courroux.
6 “Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
Et moi, [dira-t-il], j'ai sacré mon Roi sur Sion, la montagne de ma Sainteté.
7 Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
Je vous réciterai quel a été ce sacre; l'Eternel m'a dit: tu es mon Fils, je t'ai aujourd'hui engendré.
8 Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
Demande-moi, et je te donnerai pour ton héritage les nations, et pour ta possession les bouts de la terre.
9 Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
Tu les briseras avec un sceptre de fer, et tu les mettras en pièces comme un vaisseau de potier.
10 Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
Maintenant donc, ô Rois! ayez de l'intelligence; Juges de la terre, recevez instruction.
11 Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
Servez l'Eternel avec crainte, et égayez-vous avec tremblement.
12 Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
Baisez le Fils, de peur qu'il ne s'irrite, et que vous ne périssiez dans cette conduite, quand sa colère s'embrasera tant soit peu. Ô que bienheureux sont tous ceux qui se confient en lui!

< Zabura 2 >