< Zabura 2 >

1 Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
D'où vient que les nations ont frémi et que les peuples ont médité de vains complots?
2 Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
Les rois de la terre se sont levés, et les chefs se sont réunis ensemble contre le Seigneur et contre son Christ; (Interlude)
3 Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
Rompons leurs liens, rejetons loin de nous leur joug.
4 Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
Celui qui habite aux cieux s'en rira, et le Seigneur se moquera d'eux.
5 Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
Alors il leur parlera dans sa colère; et il les troublera dans sa fureur.
6 “Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
Mais moi, il m'a institué roi de Sion, sa sainte montagne,
7 Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
Et j'annonce les préceptes du Seigneur. Le Seigneur m'a dit: Tu es mon fils; aujourd'hui je t'ai engendré.
8 Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
Demande-moi, et je te donnerai les nations pour héritage, et pour ta possession les limites de la terre.
9 Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
Tu les gouverneras avec une verge de fer; tu les briseras comme un vaisseau d'argile.
10 Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
Et maintenant, rois, comprenez; instruisez-vous, juges de la terre.
11 Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
Servez le Seigneur avec crainte, et réjouissez-vous en lui avec tremblement.
12 Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
Embrassez sa discipline, de peur que le Seigneur ne s'irrite, et que vous ne périssiez hors de la voie juste. Lorsque soudain s'enflammera sa colère, heureux sont ceux qui ont confiance en lui!

< Zabura 2 >