< Zabura 2 >
1 Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
Why have the Gentiles been seething, and why have the people been pondering nonsense?
2 Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
The kings of the earth have stood up, and the leaders have joined together as one, against the Lord and against his Christ:
3 Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
“Let us shatter their chains and cast their yoke away from us.”
4 Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
He who dwells in heaven will ridicule them, and the Lord will mock them.
5 Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
Then will he speak to them in his anger and trouble them with his fury.
6 “Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
Yet I have been appointed king by him over Zion, his holy mountain, preaching his precepts.
7 Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
The Lord has said to me: You are my son, this day have I begotten you.
8 Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
Ask of me and I will give to you: the Gentiles for your inheritance, and the ends of the earth for your possession.
9 Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
You will rule them with an iron rod, and you will shatter them like a potter’s vessel.
10 Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
And now, O kings, understand. Receive instruction, you who judge the earth.
11 Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
Serve the Lord in fear, and exult in him with trembling.
12 Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
Embrace discipline, lest at any time the Lord might become angry, and you would perish from the way of the just. Though his wrath can flare up in a short time, blessed are all those who trust in him.