< Zabura 2 >

1 Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
Therefore did the heathen rage, and the nations imagine vain things?
2 Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
The kings of the earth stood up, and the rulers gathered themselves together, against the Lord, and against his Christ;
3 Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
[saying], Let us break through their bonds, and cast away their yoke from us.
4 Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
He that dwells in the heavens shall laugh them to scorn, and the Lord shall mock them.
5 Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
Then shall he speak to them in his anger, and trouble them in his fury.
6 “Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
But I have been made king by him on Sion his holy mountain,
7 Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
declaring the ordinance of the Lord: the Lord said to me, You are my Son, today have I begotten you.
8 Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
Ask of me, and I will give you the heathen [for] your inheritance, and the ends of the earth [for] your possession.
9 Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
You shall rule them with a rod of iron; you shall dash them in pieces as a potter's vessel.
10 Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
Now therefore understand, you kings: be instructed, all you that judge the earth.
11 Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
Serve the Lord with fear, and rejoice in him with trembling.
12 Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
Accept correction, lest at any time the Lord be angry, and you should perish from the righteous way: whenever his wrath shall be suddenly kindled, blessed are all they that trust in him.

< Zabura 2 >