< Zabura 2 >
1 Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
Hvorfor fnyse Hedningerne, og grunde Folkene paa Forfængelighed?
2 Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
Jordens Konger rejse sig, og Fyrsterne raadslaa tilsammen imod Herren og imod hans salvede:
3 Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
„Lader os sønderrive deres Baand og kaste deres Reb af os!”
4 Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
Han, som bor i Himlene, ler; Herren spotter dem.
5 Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
Da skal han tale til dem i sin Vrede og forfærde dem i sin Harme:
6 “Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
„Jeg har dog indsat min Konge over Zion, mit hellige Bjerg.”
7 Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
Jeg vil fortælle om et beskikket Raad; Herren sagde til mig: Du er min Søn; jeg fødte dig i Dag.
8 Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
Begær af mig, saa vil jeg give dig Hedningerne til din Arv og Jordens Grænser til din Ejendom.
9 Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
Du skal sønderslaa dem med et Jernspir, ligesom Pottemagerkar skal du sønderbryde dem.
10 Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
Og nu, I Konger, handler klogelig! lader eder undervise, I Dommere paa Jorden!
11 Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
Tjener Herren med Frygt og fryder eder med Bæven!
12 Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
Kysser Sønnen, at han ikke bliver vred, og I skulle omkomme paa Vejen; thi om et lidet vil hans Vrede optændes; salige alle de, som forlade sig paa ham!