< Zabura 19 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sammai suna shelar ɗaukakar Allah; sararin sama suna furta aikin hannuwansa.
برای رهبر سرایندگان. مزمور داوود. آسمان از شکوه و عظمت خدا حکایت می‌کند و صنعت دستهای او را نشان می‌دهد.
2 Kowace rana tana yin jawabi; kowane dare yana nuna sani.
روز و شب حکمت خدا را اعلام می‌کنند.
3 Ba magana, ba kalmar da aka hurta, ba wani amon da aka ji daga gare su.
بی سر و صدا سخن می‌گویند، و آوازشان شنیده نمی‌شود؛
4 Duk da haka muryarsu tana kaiwa ga dukan duniya, kalmominsu zuwa iyakokin duniya. A sammai Allah ya kafa tenti domin rana,
با این همه، پیامشان به سراسر زمین منتشر می‌گردد، و کلامشان تا به کرانهای جهان می‌رسد. خدا خیمه‌ای در آسمان برای خورشید بر پا کرده است.
5 wanda yake kamar ango mai fitowa daga rumfarsa, kamar gwani ɗan wasan da yake farin ciki yă yi tsere.
خورشید مانند تازه داماد، با خوشحالی از حجله بیرون می‌آید و مانند پهلوان شادمانه در میدان می‌دود.
6 Takan taso daga ƙarshen sammai ta kewaye zuwa wancan; babu abin da yake ɓuya wa zafinta.
از یک سوی آسمان به سوی دیگر می‌شتابد، و حرارتش همه جا را فرا می‌گیرد.
7 Dokar Ubangiji cikakkiya ce, takan wartsakar da rai. Farillan Ubangiji abin dogara ne, suna mai da hikima da sauƙi.
احکام خداوند کامل است و جان را تازه می‌سازد، کلام خداوند قابل اعتماد است و به ساده‌دلان حکمت می‌بخشد.
8 Ƙa’idodin Ubangiji daidai ne, suna ba da farin ciki ga zuciya. Umarnan Ubangiji haske ne suna ba da haske ga idanu.
فرامین خداوند راست است و دل را شاد می‌سازد، اوامر خداوند پاک است و بصیرت می‌بخشد.
9 Tsoron Ubangiji yakan kawo tsabtar zuciya, zai kasance har abada. Farillan Ubangiji tabbatattu ne, kuma gaba ɗaya masu adalci ne.
قوانین خداوند قابل احترام و نیکوست و تا ابد برقرار می‌ماند. احکام خداوند تماماً حق و عدل است،
10 Sun fi zinariya daraja, fiye da zalla zinariya nesa; sun fi zuma zaƙi fiye da zuma daga kaki.
از طلای ناب مرغوبتر و از عسل خالص شیرینتر.
11 Ta wurinsu ana gargaɗe bawanka; a kiyaye su akwai lada mai girma.
احکام تو، بنده‌ات را آگاه و هوشیار می‌سازد و هر که آنها را بجا آورد، پاداش عظیمی خواهد یافت.
12 Wane ne zai iya rabe kurakuransa? Ya gafarta ɓoyayyun laifofinsa.
کیست که بتواند به گناهان نهان خود پی ببرد؟ خداوندا، تو مرا از چنین گناهان پاک ساز!
13 Ka kiyaye bawanka daga zunubin ganganci; kada ka bari su yi mulki a kaina. Ta haka zan zama marar laifi; marar laifi na babban tawaye.
و نیز مرا از گناهان عمدی بازدار و نگذار بر من مسلط شوند. آنگاه خواهم توانست از شر گناه آزاد شده، بی‌عیب باشم.
14 Bari kalmomin bakina da tunanin zuciyata su zama abin gamsuwa a gabanka, Ya Ubangiji, Dutsena da Mai fansata.
ای خداوند، ای پناهگاه و نجا‌ت‌دهندۀ من، سخنان دهانم و تفکر دلم مورد پسند تو باشند.

< Zabura 19 >