< Zabura 19 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sammai suna shelar ɗaukakar Allah; sararin sama suna furta aikin hannuwansa.
Jusqu'à la Fin, psaume de David. Les cieux racontent la gloire du Seigneur, et le firmament fait connaître l'œuvre de ses mains.
2 Kowace rana tana yin jawabi; kowane dare yana nuna sani.
Le jour parle de lui au jour; la nuit montre sa science à la nuit.
3 Ba magana, ba kalmar da aka hurta, ba wani amon da aka ji daga gare su.
Il n'y a langage ni paroles dont leur voix ne soit entendue.
4 Duk da haka muryarsu tana kaiwa ga dukan duniya, kalmominsu zuwa iyakokin duniya. A sammai Allah ya kafa tenti domin rana,
Leur voix s'est répandue sur toute la terre; leur parole est parvenue au bout du monde. Il a tendu son tabernacle dans le soleil;
5 wanda yake kamar ango mai fitowa daga rumfarsa, kamar gwani ɗan wasan da yake farin ciki yă yi tsere.
Et le soleil ressemble au jeune époux sortant de son lit nuptial, il a tressailli de joie comme un géant pour courir dans sa voie.
6 Takan taso daga ƙarshen sammai ta kewaye zuwa wancan; babu abin da yake ɓuya wa zafinta.
Il sort de l'extrémité du ciel; et son issue est à l'autre extrémité; et nul ne peut se mettre à l'abri de sa chaleur.
7 Dokar Ubangiji cikakkiya ce, takan wartsakar da rai. Farillan Ubangiji abin dogara ne, suna mai da hikima da sauƙi.
La loi du Seigneur est immaculée, elle convertit les âmes; le témoignage du Seigneur est fidèle, il donne la sagesse aux enfants.
8 Ƙa’idodin Ubangiji daidai ne, suna ba da farin ciki ga zuciya. Umarnan Ubangiji haske ne suna ba da haske ga idanu.
La justice du Seigneur est droite, elle réjouit le cœur; les préceptes du Seigneur brillent d'un vif éclat, ils éclairent les yeux.
9 Tsoron Ubangiji yakan kawo tsabtar zuciya, zai kasance har abada. Farillan Ubangiji tabbatattu ne, kuma gaba ɗaya masu adalci ne.
La crainte du Seigneur est sainte, elle persiste dans les siècles des siècles; les jugements du Seigneur sont vrais, et justifiés en eux-mêmes.
10 Sun fi zinariya daraja, fiye da zalla zinariya nesa; sun fi zuma zaƙi fiye da zuma daga kaki.
Ils sont infiniment plus désirables que l'or et les pierres précieuses; ils sont plus doux que le miel et que les rayons de miel.
11 Ta wurinsu ana gargaɗe bawanka; a kiyaye su akwai lada mai girma.
Aussi ton serviteur les garde-t-il; à les garder on gagne un riche salaire.
12 Wane ne zai iya rabe kurakuransa? Ya gafarta ɓoyayyun laifofinsa.
Qui a conscience de ses chutes? Purifies-moi de mes fautes les plus cachées.
13 Ka kiyaye bawanka daga zunubin ganganci; kada ka bari su yi mulki a kaina. Ta haka zan zama marar laifi; marar laifi na babban tawaye.
Préserve ton serviteur des vices des étrangers. S'ils ne me dominent pas, alors je serai sans souillure et lavé d'un grand péché.
14 Bari kalmomin bakina da tunanin zuciyata su zama abin gamsuwa a gabanka, Ya Ubangiji, Dutsena da Mai fansata.
Alors les paroles de ma bouche te plairont, et les pensées de mon cœur seront toujours agréables devant toi. Seigneur, tu es mon aide et mon Rédempteur.