< Zabura 19 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sammai suna shelar ɗaukakar Allah; sararin sama suna furta aikin hannuwansa.
[When people look at everything that] God [has placed in] the skies, they can see that he is very great; they can see the great things that he has created.
2 Kowace rana tana yin jawabi; kowane dare yana nuna sani.
Day after day [it is as though the sun] proclaims [the glory of God], and night after night [it is as though the moon and stars] say that they know [that God made them].
3 Ba magana, ba kalmar da aka hurta, ba wani amon da aka ji daga gare su.
They do not really speak; they do not say any words. There is no voice [from them] for anyone to hear.
4 Duk da haka muryarsu tana kaiwa ga dukan duniya, kalmominsu zuwa iyakokin duniya. A sammai Allah ya kafa tenti domin rana,
But what they declare [about God] goes throughout the world, and [even people who live in] the most distant/remote places on earth can know it. The sun is in the skies where God placed it [MET];
5 wanda yake kamar ango mai fitowa daga rumfarsa, kamar gwani ɗan wasan da yake farin ciki yă yi tsere.
it rises each morning like a bridegroom [who is happy] as he comes out of his bedroom after his wedding. It is like a strong athlete who is very eager to start running in a race.
6 Takan taso daga ƙarshen sammai ta kewaye zuwa wancan; babu abin da yake ɓuya wa zafinta.
The sun rises at one side of the sky and goes across [the sky and sets on] the other side, and nothing can hide from its heat.
7 Dokar Ubangiji cikakkiya ce, takan wartsakar da rai. Farillan Ubangiji abin dogara ne, suna mai da hikima da sauƙi.
The instructions that Yahweh has given us are perfect; they (revive us/give us new strength). We can be sure that the things that Yahweh has told us will never change, and [by learning them] people who have not been previously taught/instructed will become wise.
8 Ƙa’idodin Ubangiji daidai ne, suna ba da farin ciki ga zuciya. Umarnan Ubangiji haske ne suna ba da haske ga idanu.
Yahweh’s laws are fair/just; [when we obey them], we become joyful. The commands of Yahweh are clear, and [by reading them] [PRS] we start to understand [how God wants us to behave].
9 Tsoron Ubangiji yakan kawo tsabtar zuciya, zai kasance har abada. Farillan Ubangiji tabbatattu ne, kuma gaba ɗaya masu adalci ne.
It is good for people to revere Yahweh; that is something that they will do forever. What Yahweh has decided is fair, and it is always right.
10 Sun fi zinariya daraja, fiye da zalla zinariya nesa; sun fi zuma zaƙi fiye da zuma daga kaki.
The things that God has decided are more valuable than gold, even the finest/purest gold. They are sweeter than honey that drips from honeycombs.
11 Ta wurinsu ana gargaɗe bawanka; a kiyaye su akwai lada mai girma.
Furthermore, [by reading them] I learn [what things are good to do and what things are evil], and they promise a great reward to [us who] obey them.
12 Wane ne zai iya rabe kurakuransa? Ya gafarta ɓoyayyun laifofinsa.
But there is no one who can know all his errors [RHQ]; so Yahweh, forgive me for these things which I do that I do not realize are wrong.
13 Ka kiyaye bawanka daga zunubin ganganci; kada ka bari su yi mulki a kaina. Ta haka zan zama marar laifi; marar laifi na babban tawaye.
Keep me from doing things that I know are wrong; do not let my sinful desires control me. If you do that, I will no longer be guilty for committing such sins, and I will not commit the great sin [of rebelling terribly] against you.
14 Bari kalmomin bakina da tunanin zuciyata su zama abin gamsuwa a gabanka, Ya Ubangiji, Dutsena da Mai fansata.
O Yahweh, you are [like] an [overhanging] rock [MET] under which I can be safe; you are the one who protects me. I hope/desire that the things that I say and what I think will [always] please you.

< Zabura 19 >