< Zabura 19 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sammai suna shelar ɗaukakar Allah; sararin sama suna furta aikin hannuwansa.
(Til sangmesteren. En salme af David.) Himlen forkynder Guds Ære, Hvælvingen kundgør hans Hænders værk.
2 Kowace rana tana yin jawabi; kowane dare yana nuna sani.
Dag bærer Bud til Dag, Nat lader Nat det vide.
3 Ba magana, ba kalmar da aka hurta, ba wani amon da aka ji daga gare su.
Uden Ord og uden Tale, uden at Lyden høres,
4 Duk da haka muryarsu tana kaiwa ga dukan duniya, kalmominsu zuwa iyakokin duniya. A sammai Allah ya kafa tenti domin rana,
når Himlens Røst over Jorden vide, dens Tale til Jorderigs Ende. På Himlen rejste han Solen et Telt;
5 wanda yake kamar ango mai fitowa daga rumfarsa, kamar gwani ɗan wasan da yake farin ciki yă yi tsere.
som en Brudgom går den ud af sit Kammer, er glad som en Helt ved at løbe sin Bane,
6 Takan taso daga ƙarshen sammai ta kewaye zuwa wancan; babu abin da yake ɓuya wa zafinta.
rinder op ved Himlens ene Rand, og dens Omløb når til den anden. Intet er skjult for dens Glød.
7 Dokar Ubangiji cikakkiya ce, takan wartsakar da rai. Farillan Ubangiji abin dogara ne, suna mai da hikima da sauƙi.
HERRENs Lov er fuldkommen, kvæger Sjælen, HERRENs Vidnesbyrd holder, gør enfoldig viis,
8 Ƙa’idodin Ubangiji daidai ne, suna ba da farin ciki ga zuciya. Umarnan Ubangiji haske ne suna ba da haske ga idanu.
HERRENs Forskrifter er rette, glæder Hjertet, HERRENs Bud er purt, giver Øjet Glans,
9 Tsoron Ubangiji yakan kawo tsabtar zuciya, zai kasance har abada. Farillan Ubangiji tabbatattu ne, kuma gaba ɗaya masu adalci ne.
HERRENs Frygt er ren, varer evigt, HERRENs Lovbud er Sandhed, rette til Hobe,
10 Sun fi zinariya daraja, fiye da zalla zinariya nesa; sun fi zuma zaƙi fiye da zuma daga kaki.
kostelige fremfor Guld, ja fint Guld i Mængde, søde fremfor Honning og Kubens Saft.
11 Ta wurinsu ana gargaɗe bawanka; a kiyaye su akwai lada mai girma.
Din Tjener tager og Vare på dem; at holde dem lønner sig rigt.
12 Wane ne zai iya rabe kurakuransa? Ya gafarta ɓoyayyun laifofinsa.
Hvo mærker selv, at han fejler? Tilgiv mig lønlige Brøst!
13 Ka kiyaye bawanka daga zunubin ganganci; kada ka bari su yi mulki a kaina. Ta haka zan zama marar laifi; marar laifi na babban tawaye.
Værn også din Tjener mod frække, ej råde de over mig! Så bliver jeg uden Lyde og fri for svare Synder.
14 Bari kalmomin bakina da tunanin zuciyata su zama abin gamsuwa a gabanka, Ya Ubangiji, Dutsena da Mai fansata.
Lad min Munds Ord være dig til Behag, lad mit Hjertes Tanker nå frem for dit Åsyn, HERRE, min Klippe og min Genløser!

< Zabura 19 >