< Zabura 18 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
Al Músico principal: Salmo de David, siervo de Jehová, el cual profirió á Jehová las palabras de este cántico el día que le libró Jehová de mano de todos sus enemigos, y de mano de Saúl. Entonces dijo: AMARTE he, oh Jehová, fortaleza mía.
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
Jehová, roca mía y castillo mío, y mi libertador; Dios mío, fuerte mío, en él confiaré; escudo mío, y el cuerno de mi salud, mi refugio.
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
Invocaré á Jehová, digno de ser alabado, y seré salvo de mis enemigos.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
Cercáronme dolores de muerte, y torrentes de perversidad me atemorizaron.
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
Dolores del sepulcro me rodearon, previniéronme lazos de muerte. (Sheol )
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
En mi angustia invoqué á Jehová, y clamé á mi Dios: él oyó mi voz desde su templo, y mi clamor llegó delante de él, á sus oídos.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
Y la tierra fué conmovida y tembló; y moviéronse los fundamentos de los montes, y se estremecieron, porque se indignó él.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Humo subió de su nariz, y de su boca consumidor fuego; carbones fueron por él encendidos.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
Y bajó los cielos, y descendió; y oscuridad debajo de sus pies.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
Y cabalgó sobre un querubín, y voló: voló sobre las alas del viento.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
Puso tinieblas por escondedero suyo, su pabellón en derredor de sí; oscuridad de aguas, nubes de los cielos.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
Por el resplandor delante de él, sus nubes pasaron; granizo y carbones ardientes.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
Y tronó en los cielos Jehová, y el Altísimo dió su voz; granizo y carbones de fuego.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
Y envió sus saetas, y desbaratólos; y echó relámpagos, y los destruyó.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
Y aparecieron las honduras de las aguas, y descubriéronse los cimientos del mundo, á tu reprensión, oh Jehová, por el soplo del viento de tu nariz.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
Envió desde lo alto; tomóme, sacóme de las muchas aguas.
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
Libróme de mi poderoso enemigo, y de los que me aborrecían, aunque eran ellos más fuertes que yo.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
Asaltáronme en el día de mi quebranto: mas Jehová fué mi apoyo.
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
Y sacóme á anchura: libróme, porque se agradó de mí.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
Hame pagado Jehová conforme á mi justicia: conforme á la limpieza de mis manos me ha vuelto.
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
Porque yo he guardado los caminos de Jehová, y no me aparté impíamente de mi Dios.
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
Pues todos sus juicios estuvieron delante de mí, y no eché de mí sus estatutos.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
Y fuí íntegro para con él, y cauteléme de mi maldad.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Pagóme pues Jehová conforme á mi justicia; conforme á la limpieza de mis manos delante de sus ojos.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
Con el misericordioso te mostrarás misericordioso, y recto para con el hombre íntegro.
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
Limpio te mostrarás para con el limpio, y severo serás para con el perverso.
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
Y tú salvarás al pueblo humilde, y humillarás los ojos altivos.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
Tú pues alumbrarás mi lámpara: Jehová mi Dios alumbrará mis tinieblas.
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
Porque contigo desharé ejércitos; y con mi Dios asaltaré muros.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
Dios, perfecto su camino: es acendrada la palabra de Jehová: escudo es á todos los que en él esperan.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
Porque ¿qué Dios hay fuera de Jehová? ¿y qué fuerte fuera de nuestro Dios?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
Dios es el que me ciñe de fuerza, é hizo perfecto mi camino;
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
Quien pone mis pies como [pies] de ciervas, é hízome estar sobre mis alturas;
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Quien enseña mis manos para la batalla, y será quebrado con mis brazos el arco de acero.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
Dísteme asimismo el escudo de tu salud: y tu diestra me sustentó, y tu benignidad me ha acrecentado.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Ensanchaste mis pasos debajo de mí, y no titubearon mis rodillas.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
Perseguido he mis enemigos, y alcancélos, y no volví hasta acabarlos.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
Helos herido, y no podrán levantarse: cayeron debajo de mis pies.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
Pues me ceñiste de fortaleza para la pelea; has agobiado mis enemigos debajo de mí.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
Y dísteme la cerviz de mis enemigos, y destruí á los que me aborrecían.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
Clamaron, y no hubo quien salvase: [aun] á Jehová, mas no los oyó.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
Y molílos como polvo delante del viento; esparcílos como lodo de las calles.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Librásteme de contiendas de pueblo: pusísteme por cabecera de gentes: pueblo que yo no conocía, me sirvió.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
Así que hubo oído, me obedeció; los hijos de extraños me mintieron;
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
Los extraños flaquearon, y tuvieron miedo desde sus encerramientos.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
Viva Jehová, y sea bendita mi roca; y ensalzado sea el Dios de mi salud:
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
El Dios que me da las venganzas, y sujetó pueblos á mí.
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
Mi libertador de mis enemigos: hicísteme también superior de mis adversarios; librásteme de varón violento.
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
Por tanto yo te confesaré entre las gentes, oh Jehová, y cantaré á tu nombre.
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
El cual engrandece las saludes de su rey, y hace misericordia á su ungido, á David y á su simiente, para siempre.