< Zabura 18 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
Љубићу Те, Господе, крепости моја,
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
Господе, Граде мој, Заклоне мој, који се оборити не може, Избавитељу мој, Боже мој, Камена горо, на којој се не бојим зла, Штите мој, Роже спасења мог, Уточиште моје!
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
Призивам Господа, коме се клањати ваља, и опраштам се непријатеља својих.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
Обузеше ме смртне болести, и потоци неваљалих људи уплашише ме.
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
Опколише ме болести паклене, стегоше ме замке смртне. (Sheol )
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
У својој тескоби призвах Господа, и к Богу свом повиках; Он чу из двора свог глас мој, и вика моја дође Му до ушију.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
Затресе се и поколеба се земља, задрмаше се и померише из темеља горе, јер се Он разљути.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Подиже се дим од гнева Његовог, из уста Његових огањ, који прождире и живо угљевље одскакаше од Њега.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
Сави небеса и сиђе. Мрак беше под ногама Његовим.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
Седе на херувима и подиже се, и полете на крилима ветреним.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
Од мрака начини себи кров, сеницу око себе, од мрачних вода, облака ваздушних.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
Од севања пред Њим кроз облаке Његове удари град и живо угљевље.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
Загрме на небесима Господ, и Вишњи пусти глас свој, град и живо угљевље.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
Пусти стреле своје, и разметну их; силу муња, и расу их.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
И показаше се извори водени, и открише се темељи васиљени од претње Твоје, Господе, од дихања духа гнева Твог.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
Тада пружи с висине руку, ухвати ме, извуче ме из воде велике.
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
Избави ме од непријатеља мог силног и од мојих ненавидника, кад беху јачи од мене.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
Усташе на ме у дан невоље моје, али ми Господ би потпора.
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
Изведе ме на пространо место, и избави ме, јер сам Му мио.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
Даде ми Господ по правди мојој, и за чистоту руку мојих дарива ме.
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
Јер се држах путева Господњих, и не одметнух се Бога свог,
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
Него су сви закони Његови преда мном, и заповести Његове не уклањам од себе.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
Бих Му веран, и чувах се од безакоња свог.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Даде ми Господ по правди мојој, по чистоти руку мојих пред очима Његовим.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
Са светима поступаш свето, с човеком верним верно,
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
С чистим чисто, а с неваљалим насупрот њему.
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
Јер Ти помажеш људима невољним, а очи поносите понижаваш.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
Ти распаљујеш видело моје; Господ мој просветљује таму моју.
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
С Тобом разбијам војску, и с Богом својим скачем преко зида.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
Пут је Господњи веран, реч Господња чиста. Он је штит свима који се у Њ уздају.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
Јер ко је Бог осим Господа, и ко је одбрана осим Бога нашег?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
Овај Бог опасује ме снагом, и чини ми веран пут.
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
Даје ми ноге као у јелена, и на висине ставља ме.
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Учи руке моје боју, и мишице моје чини да су лук од бронзе.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
Ти ми дајеш штит спасења свог; десница Твоја држи ме, и милост Твоја чини ме велика.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Ти шириш корак мој, те се не спотичу ноге моје.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
Терам непријатеље своје и стижем их, и не враћам се док их не истребим.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
Обарам их, и не могу устати, падају под ноге моје.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
Јер ме Ти опасујеш снагом за бој, и који устану на ме, обараш их преда мном.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
Непријатеља мојих плећи Ти ми обраћаш, и потирем ненавиднике своје.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
Они вичу, али немају помагача, ка Господу, али их Он не слуша.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
Расипам их као прах по ветру, као блато по улицама газим их.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Ти ме избављаш од буне народне, постављаш ме да сам глава туђим племенима; народ ког не познавах, служи ми.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
По самом чувењу слушају ме, туђини покорни су ми.
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
Туђини бледе, дрхћу у градовима својим.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
Жив је Господ, и да је благословен бранич мој! Да се узвиси Бог спасења мог,
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
Бог, који ми даје освету, и покорава ми народе,
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
Који ме избавља од непријатеља, подиже ме над оне који устају на ме и од човека жестоког избавља ме!
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
Тога ради хвалим Те, Господе, пред народима, и певам имену Твом,
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
Који славно избављаш цара свог, и чиниш милост помазанику свом Давиду и наслеђу његовом довека.