< Zabura 18 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
Ljubiæu te, Gospode, krjeposti moja,
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
Gospode, grade moj, zaklone moj, koji se oboriti ne može, izbavitelju moj, Bože moj, kamena goro, na kojoj se ne bojim zla, štite moj, rože spasenja mojega, utoèište moje!
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
Prizivljem Gospoda, kojemu se klanjati valja, i opraštam se neprijatelja svojih.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
Obuzeše me smrtne bolesti, i potoci nevaljalijeh ljudi uplašiše me.
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
Opkoliše me bolesti paklene, stegoše me zamke smrtne. (Sheol )
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
U svojoj tjeskobi prizvah Gospoda, i k Bogu svojemu povikah; on èu iz dvora svojega glas moj, i vika moja doðe mu do ušiju.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
Zatrese se i pokoleba se zemlja, zadrmaše se i pomjeriše iz temelja gore, jer se on razljuti.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Podiže se dim od gnjeva njegova, iz usta njegovijeh oganj, koji proždire, i živo ugljevlje otskakaše od njega.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
Savi nebesa i siðe. Mrak bješe pod nogama njegovijem.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
Sjede na heruvima i podiže se, i poletje na krilima vjetrnijem.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
Od mraka naèini sebi krov, sjenicu oko sebe, od mraènijeh voda, oblaka vazdušnijeh.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
Od sijevanja pred njim kroz oblake njegove udari grad i živo ugljevlje.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
Zagrmje na nebesima Gospod, i višnji pusti glas svoj, grad i živo ugljevlje.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
Pusti strijele svoje, i razmetnu ih; silu munja, i rasu ih.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
I pokazaše se izvori vodeni, i otkriše se temelji vasionoj od prijetnje tvoje, Gospode, od dihanja duha gnjeva tvojega.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
Tada pruži s visine ruku, uhvati me, izvuèe me iz vode velike.
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
Izbavi me od neprijatelja mojega silnoga i od mojih nenavidnika, kad bijahu jaèi od mene.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
Ustaše na me u dan nevolje moje, ali mi Gospod bi potpora.
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
Izvede me na prostrano mjesto, i izbavi me, jer sam mu mio.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
Dade mi Gospod po pravdi mojoj, i za èistotu ruku mojih dariva me.
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
Jer se držah putova Gospodnjih, i ne odmetnuh se Boga svojega,
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
Nego su svi zakoni njegovi preda mnom, i zapovijesti njegovijeh ne uklanjam od sebe.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
Bih mu vjeran, i èuvah se od bezakonja svojega.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Dade mi Gospod po pravdi mojoj, po èistoti ruku mojih pred oèima njegovima.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
Sa svetima postupaš sveto, s èovjekom vjernim vjerno,
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
S èistim èisto, a s nevaljalim nasuprot njemu.
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
Jer ti pomažeš ljudima nevoljnim, a oèi ponosite ponižavaš.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
Ti raspaljuješ vidjelo moje; Gospod moj prosvjetljuje tamu moju.
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
S tobom razbijam vojsku, i s Bogom svojim skaèem preko zida.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
Put je Božji vjeran, rijeè Gospodnja èista. On je štit svjema koji se u nj uzdaju.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
Jer ko je Bog osim Gospoda, i ko je obrana osim Boga našega?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
Ovaj Bog opasuje me snagom, i èini mi vjeran put.
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
Daje mi noge kao u jelena, i na visine stavlja me.
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Uèi ruke moje boju, i mišice moje èini da su luk od mjedi.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
Ti mi daješ štit spasenja svojega; desnica tvoja drži me, i milost tvoja èini me velika.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Ti širiš korak moj, te se ne spotièu noge moje.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
Tjeram neprijatelje svoje i stižem ih, i ne vraæam se dok ih ne istrijebim.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
Obaram ih, i ne mogu ustati, padaju pod noge moje.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
Jer me ti opasuješ snagom za boj, i koji ustanu na me, obaraš ih preda mnom.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
Neprijatelja mojih pleæi ti mi obraæaš, i potirem nenavidnike svoje.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
Oni vièu, ali nema pomagaèa, ka Gospodu, ali ih on ne sluša.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
Rasipam ih kao prah po vjetru, kao blato po ulicama gazim ih.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Ti me izbavljaš od bune narodne, postavljaš me da sam glava tuðim plemenima; narod kojega ne poznavah, služi mi.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
Po samome èuvenju slušaju me, tuðini pokorni su mi.
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
Tuðini blijede, dršæu u gradovima svojim.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
Živ je Gospod, i da je blagosloven braniè moj! Da se uzvisi Bog spasenja mojega,
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
Bog, koji mi daje osvetu, i pokorava mi narode,
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
Koji me izbavlja od neprijatelja, podiže me nad one koji ustaju na me i od èovjeka žestoka izbavlja me!
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
Toga radi hvalim te, Gospode, pred narodima, i pojem imenu tvojemu,
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
Koji slavno izbavljaš cara svojega, i èiniš milost pomazaniku svojemu Davidu i natražju njegovu dovijeka.