< Zabura 18 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
伶長にうたはしめたるヱホバの僕ダビデの歌、このうたの詞はもろもろの仇およびサウルの手より救れしときヱホバに對ひてうたへるなり 云く ヱホバわれの力よ われ切になんぢを愛しむ
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
ヱホバはわが巌 わが城 われをすくふ者 わがよりたのむ神 わが堅固なるいはほ わが盾 わがすくひの角 わがたかき櫓なり
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
われ讃稱ふべきヱホバをよびて仇人よりすくはるることをえん
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
死のつな我をめぐり惡のみなぎる流われをおそれしめたり
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol h7585)
陰間のなは我をかこみ死のわな我にたちむかへり (Sheol h7585)
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
われ窮苦のうちにありてヱホバをよび又わが紳にさけびたり ヱホバはその官よりわが聲をききたまふ その前にてわがよびし聲はその耳にいれり
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
このときヱホバ怒りたまひたれば地はふるひうごき山の基はゆるぎうごきたり
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
烟その鼻よりたち火その口よりいでてやきつくし炭はこれがために燃あがれり
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
ヱホバは天をたれて臨りたまふ その足の下はくらきこと甚だし
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
かくてケルブに乗りてとび風のつばさにて翔り
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
闇をおほひとなし水のくらきとそらの密雲とをそのまはりの幕となしたまへり
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
そのみまへの光輝よりくろくもをへて雹ともえたる炭とふりきたれり
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
ヱホバは天に雷鳴をとどろかせたまへり 至上者のこゑいでて雹ともえたる炭とふりきたり
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
ヱホバ矢をとばせてかれらを打ちらし數しげき電光をはなちてかれらをうち敗りたまへり
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
ヱホバよ斯るときになんぢの叱咤となんぢの鼻のいぶきとによりて水の底みえ地の基あらはれいでたり
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
ヱホバはたかきより手をのべ我をとりて大水よりひきあげ
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
わがつよき仇とわれを憎むものとより我をたすけいだしたまへり かれらは我にまさりて最強かりき
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
かれらはわが災害の日にせまりきたれり 然どヱホバはわが支柱となりたまひき
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
ヱホバはわれを悦びたまふがゆゑにわれをたづさへ廣處にだして助けたまへり
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
ヱホバはわが正義にしたがひて恩賜をたまひ わが手のきよきにしたがひて報賞をたれたまへり
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
われヱホバの道をまもり惡をなしてわが神よりはなれしことなければなり
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
そのすべての審判はわがまへにありて われその律法をすてしことなければなり
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
われ神にむかひて缺るところなく己をまもりて不義をはなれたり
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
この故にヱホバはわがただしきとその目前にわが手のきよきとにしたがひて我にむくいをなし給へり
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
なんぢ憐憫あるものには憐みあるものとなり完全ものには全きものとなり
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
きよきものには潔きものとなり僻むものにはひがむ者となりたまふ
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
そは汝くるしめる民をすくひたまへど高ぶる目をひくくしたまふ可ればなり
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
なんぢわが燈火をともし給ふべければなり わが神ヱホバわが暗をてらしたまはん
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
我なんぢによりて軍の中をはせとほり わが神によりて垣ををどりこゆ
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
神はしもその途またくヱホバの言はきよし ヱホバはずべて依頼むものの盾なり
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
そはヱホバのほかに紳はたれぞや われらの紳のほかに巌はたれぞや
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
神はちからをわれに帯しめ わが途を全きものとなしたまふ
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
神はわが足を唐のあしのごとくし我をわが高處にたたせたまふ
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
神はわが手をたたかひにならはせてわが臂に銅弓をひくことを得しめたまふ
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
又なんぢの救の盾をわれにあたへたまへり なんぢの右手われをささへなんぢの謙卑われを大ならしめたまへり
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
なんぢわが歩むところを寛濶ならしめたまひたれば わが足ふるはざりき
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
われ仇をおひてこれに追及かれらのほろぶるまでは歸ることをせじ
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
われかれらを撃てたつことを得ざらしめん かれらはわが足の下にたふるべし
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
そはなんぢ戦争のために力をわれに帯しめ われにさからひておこりたつ者をわが下にかがませたまひたればなり
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
我をにくむ者をわが滅しえんがために汝またわが仇の背をわれにむけしめ給へり
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
かれら叫びたれども救ふものなく ヱホバに對ひてさけびたれども答へたまはざりき
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
我かれらを風のまへの塵のごとくに搗砕き ちまたの坭のごとくに打棄たり
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
なんぢわれを民のあらそひより助けいだし我をたててもろもろの國の長となしたまへり わがしらざる民われにつかへん
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
かれらわが事をききて立刻われにしたがひ異邦人はきたりて佞りつかへん
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
ことくにびとは衰へてその城よりをののきいでん
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
ヱホバは活ていませり わが磐はほむべきかな わがすくひの神はあがむべきかな
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
わがために讎をむくい異邦人をわれに服はせたまふはこの神なり
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
神はわれを仇よりすくひたまふ實になんぢは我にさからひて起りたつ者のうへに我をあげ あらぶる人より我をたすけいだし給ふ
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
この故にヱホバよ われもろもろの國人のなかにてなんぢに感謝し なんぢの名をほめうたはん
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
ヱホバはおほいなる救をその王にあたへ その受膏者ダビデとその裔とに世々かぎりなく憐憫をたれたまふ

< Zabura 18 >