< Zabura 18 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
Untuk pemimpin kor. Mazmur Daud, hamba TUHAN. Dinyanyikan kepada TUHAN pada waktu Daud dilepaskan dari Saul dan dari musuh-musuhnya. Kucinta kepada-Mu, ya TUHAN, Engkaulah kekuatanku.
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
TUHAN seperti benteng yang kuat tempat aku berlindung. Allahku seperti gunung batu tempat aku bernaung. Seperti perisai Ia menutupi aku, dan menjaga aku agar aman selalu.
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
Aku berseru kepada TUHAN yang patut dipuji, Ia membebaskan aku dari musuh-musuhku.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
Aku dikelilingi bahaya maut dan digenangi banjir kebinasaan.
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol h7585)
Aku dikelilingi bahaya maut, perangkap maut ada di depanku. (Sheol h7585)
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
Dalam kesesakanku aku berseru kepada TUHAN, aku berteriak kepada Allahku mohon pertolongan. Dari Rumah-Nya Ia mendengar suaraku dan memperhatikan seruanku.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
Lalu bumi berguncang dan bergetar, dasar-dasar gunung goyah dan gemetar karena kemarahan Allah.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Asap menyembur dari lubang hidung-Nya, api dan bara keluar dari mulut-Nya.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
Langit dibelah-Nya, lalu turunlah Ia dengan awan gelap di bawah kaki-Nya.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
Ia terbang dengan mengendarai kerub; Ia melayang di atas sayap angin.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
Ia menyelubungi diri-Nya dengan kegelapan; awan mendung yang tebal mengelilingi Dia.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
Dari kilat di hadapan-Nya, keluarlah awan, hujan es dan api.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
Lalu TUHAN mengguntur dari angkasa; Yang Mahatinggi memperdengarkan suara-Nya.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
Ia menembakkan panah-panah-Nya dan menceraiberaikan musuh; Ia menyambarkan kilat berulang-ulang, dan membuat mereka lari.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
Dasar laut tersingkap dan alas bumi terbuka waktu TUHAN membentak musuh-Nya dengan murka.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
Dari atas TUHAN mengulurkan tangan-Nya; dipegang-Nya aku dan ditarik-Nya dari air yang dalam.
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
Ia menyelamatkan aku dari musuh yang perkasa dan dari orang-orang yang membenci aku, karena mereka terlalu kuat bagiku.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
Mereka menyerang aku waktu aku ditimpa bencana, tetapi TUHAN menjadi penolongku.
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
Ia melepaskan aku dari bahaya dan menyelamatkan aku karena Ia berkenan padaku.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
TUHAN membalas perbuatanku yang benar; Ia memberkati aku sebab aku tidak bersalah.
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
Aku mentaati perintah TUHAN dan tidak berpaling dari Allahku.
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
Semua hukum-Nya kuperhatikan, perintah-perintah-Nya tidak kulalaikan.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
Ia tahu bahwa aku tidak bercela dan menjauhkan diri dari kesalahan.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Maka TUHAN membalas perbuatanku yang benar sebab Ia tahu aku tidak bersalah.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
TUHAN, Engkau setia kepada orang yang setia dan baik kepada orang yang baik.
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
Terhadap orang yang suci Kaunyatakan diri-Mu suci, tetapi orang yang jahat Kaumusuhi.
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
Orang yang rendah hati Kauselamatkan, tetapi orang yang congkak Kautundukkan.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
Engkau menyalakan pelitaku; TUHAN Allahku menerangi kegelapanku.
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
Engkau menguatkan aku untuk menumpas musuh; dengan bantuan Allahku kudobrak pertahanan mereka.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
Perbuatan Allah sempurna janji TUHAN dapat dipercaya. Ia seperti perisai bagi semua yang berlindung pada-Nya.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
Sebab hanya Tuhanlah Allah; Allah saja pembela kita.
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
Dialah Allah yang menguatkan aku dan membuat jalanku aman.
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
Ia menguatkan kakiku seperti kaki rusa, dan menjaga keselamatanku di pegunungan.
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Ia melatih aku untuk berperang, sehingga aku dapat merentangkan busur yang paling kuat.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
TUHAN, Engkau melindungi dan menyelamatkan aku, dan menopang aku dengan kuasa-Mu; aku menjadi unggul karena tindakan-Mu.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Kaujaga aku supaya aku tidak tertawan, dan aku tidak pernah jatuh.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
Kukejar musuhku dan kukalahkan mereka, dan pantang mundur sampai mereka binasa.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
Kubanting mereka sampai tak dapat bangun lagi, mereka rebah tak berdaya di depan kakiku.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
Kauberi aku kekuatan untuk berperang, dan kemenangan atas musuh-musuhku.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
Kaubuat musuhku lari daripadaku; orang-orang yang membenci aku kubinasakan.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
Mereka berteriak, tetapi tak ada yang menolong, mereka berseru kepada TUHAN, tetapi Ia tidak menjawab.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
Mereka kuremukkan seperti debu yang berhamburan, dan kusapu seperti lumpur di jalan.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Engkau membebaskan aku dari kaum yang durhaka, dan menjadikan aku penguasa bangsa-bangsa; bangsa yang tidak kukenal menjadi hambaku.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
Orang-orang asing tunduk kepadaku dan taat bila mendengar perintahku.
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
Keberanian mereka sudah hilang; mereka gemetar dan keluar dari kubunya.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
TUHAN hidup! Terpujilah pembelaku! Agungkanlah kebesaran Allah penyelamatku!
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
Ia memberi aku kemenangan atas musuhku; bangsa-bangsa ditaklukkan-Nya di hadapanku,
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
diselamatkan-Nya aku dari lawan-lawanku. TUHAN, Kauberi aku kemenangan atas musuhku, Kaulindungi aku dari orang-orang yang kejam.
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
Maka kuagungkan Engkau di antara bangsa-bangsa, dan kunyanyikan puji-pujian bagi-Mu.
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
Allah memberi kemenangan besar kepada raja-Nya, Ia tetap mengasihi orang pilihan-Nya, yaitu Daud dan keturunannya untuk selama-lamanya.

< Zabura 18 >