< Zabura 18 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
Für den Vorsänger. Von dem Knecht des HERRN, von David, welcher dem HERRN die Worte dieses Liedes sang, an dem Tage, da der HERR ihn aus der Hand aller seiner Feinde errettet hatte, auch aus der Hand Sauls. Er sprach: Ich will dich von Herzen lieben, HERR, meine Stärke!
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
Der HERR ist meine Felsenkluft, meine Burg und meine Zuflucht; mein Gott ist ein Fels, darin ich mich berge, mein Schild und das Horn meines Heils, meine Festung.
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
Den HERRN, den Hochgelobten, rief ich an und wurde von meinen Feinden errettet!
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
Todeswehen umfingen mich, Bäche Belials schreckten mich;
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol h7585)
Stricke der Unterwelt umschlangen mich, es kamen mir Todesschlingen entgegen. (Sheol h7585)
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
Da mir angst ward, rief ich den HERRN an und schrie zu meinem Gott; er hörte in seinem Tempel meine Stimme, mein Schreien vor ihm drang zu seinen Ohren.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
Die Erde bebte und erzitterte, die Grundfesten der Berge wurden erschüttert und bebten, weil er zornig war.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Rauch stieg auf von seiner Nase und verzehrendes Feuer aus seinem Munde, Feuerglut brannte daraus hervor.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
Er neigte den Himmel und fuhr herab, und Dunkel war unter seinen Füßen;
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
er fuhr auf dem Cherub und flog daher, er schwebte auf den Fittichen des Windes.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
Er machte Finsternis zu seinem Gezelt, dunkle Wasser, dichte Wolken zur Hütte um sich her.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
Aus dem Glanze vor ihm gingen seine Wolken über von Hagel und Feuerglut;
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
und der HERR donnerte im Himmel, der Höchste ließ seine Stimme erschallen, Hagel und Feuerglut.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
Und er schoß seine Pfeile und zerstreute sie, schleuderte Blitze und schreckte sie.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
Da sah man Wasserbäche, und die Gründe des Erdbodens wurden aufgedeckt von deinem Schelten, o HERR, von dem Schnauben deines grimmigen Zorns!
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
Er streckte [seine Hand] aus von der Höhe und ergriff mich, er zog mich aus großen Wassern;
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
er rettete mich von meinem mächtigen Feind und von meinen Hassern; denn sie waren mir zu stark;
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
sie hatten mich überfallen zur Zeit meines Unglücks; aber der HERR ward mir zur Stütze
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
und führte mich heraus in die Weite, er befreite mich; denn er hatte Wohlgefallen an mir.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
Der HERR vergalt mir nach meiner Gerechtigkeit, nach der Reinheit meiner Hände lohnte er mir;
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
denn ich habe die Wege des HERRN bewahrt und bin nicht abgefallen von meinem Gott,
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
sondern alle seine Verordnungen hatte ich vor Augen und stieß seine Satzungen nicht von mir,
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
und ich hielt es ganz mit ihm und hütete mich vor meiner Sünde.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Darum vergalt mir der HERR nach meiner Gerechtigkeit, nach der Reinheit meiner Hände vor seinen Augen.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
Gegen den Gütigen erzeigst du dich gütig, gegen den Rechtschaffenen rechtschaffen,
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
gegen den Reinen erzeigst du dich rein, aber den Hinterlistigen überlistest du!
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
Denn du rettest das elende Volk und erniedrigst die hohen Augen.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
Ja, du zündest meine Leuchte an; der HERR, mein Gott, macht meine Finsternis licht;
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
denn mit dir kann ich Kriegsvolk zerschmeißen und mit meinem Gott über die Mauer springen.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
Dieser Gott! Sein Weg ist vollkommen, die Rede des HERRN ist geläutert; er ist ein Schild allen, die ihm vertrauen.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
Denn wer ist Gott außer dem HERRN, und wer ist ein Fels außer unserm Gott?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
Der Gott, der mich mit Kraft umgürtete und meinen Weg unsträflich machte;
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
er machte meine Füße den Hirschen gleich und stellte mich auf meine Höhen;
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
er lehrte meine Hände streiten und meine Arme den ehernen Bogen spannen;
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
du gabst mir den Schild deines Heils, und deine Rechte stützte mich, und deine Herablassung machte mich groß;
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
du machtest mir Raum zum Gehen, daß meine Knöchel nicht wankten.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
Ich jagte meinen Feinden nach und holte sie ein und kehrte nicht um, bis sie aufgerieben waren;
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
ich zerschmetterte sie, daß sie nicht mehr aufstehen konnten; sie fielen unter meine Füße.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
Du hast mich gegürtet mit Kraft zum Streit, du hast unter mich gebeugt, die sich wider mich setzten.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
Du wandtest mir den Rücken meiner Feinde zu, und meine Hasser habe ich vertilgt.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
Sie schrieen, aber da war kein Retter; zum HERRN, aber er antwortete ihnen nicht.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
Und ich zerrieb sie zu Staub vor dem Winde, warf sie wie Kot hinaus.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Du rettetest mich aus den Zänkereien des Volkes und setztest mich zum Haupt der Heiden; ein Volk, das ich nicht kannte, dient mir;
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
sobald sie hören, folgen sie mir, die Kinder der Fremde schmeicheln mir;
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
die Kinder der Fremde verzagen und kommen zitternd aus ihren Schlössern.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
Es lebe der HERR, und gepriesen sei mein Fels, und erhoben werde der Gott meines Heils!
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
Der Gott, der mir Rache verlieh und die Völker unter mich zwang;
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
der mich meinen Feinden entrinnen ließ und mich trotz meiner Widersacher erhöhte, mich errettete von dem gewalttätigen Mann!
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
Darum will ich dich, o HERR, loben unter den Nationen und deinem Namen singen,
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
der seinem Könige große Siege verliehen hat und seinem Gesalbten Gnade erweist, David und seinem Samen bis in Ewigkeit.

< Zabura 18 >