< Zabura 18 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
Au chef des chantres. Du serviteur de l’Éternel, de David, qui adressa à l’Éternel les paroles de ce cantique, lorsque l’Éternel l’eut délivré de la main de tous ses ennemis et de la main de Saül. Il dit: Je t’aime, ô Éternel, ma force!
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
Éternel, mon rocher, ma forteresse, mon libérateur! Mon Dieu, mon rocher, où je trouve un abri! Mon bouclier, la force qui me sauve, ma haute retraite!
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
Je m’écrie: Loué soit l’Éternel! Et je suis délivré de mes ennemis.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
Les liens de la mort m’avaient environné, Et les torrents de la destruction m’avaient épouvanté;
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
Les liens du sépulcre m’avaient entouré, Les filets de la mort m’avaient surpris. (Sheol )
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
Dans ma détresse, j’ai invoqué l’Éternel, J’ai crié à mon Dieu; De son palais, il a entendu ma voix, Et mon cri est parvenu devant lui à ses oreilles.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
La terre fut ébranlée et trembla, Les fondements des montagnes frémirent, Et ils furent ébranlés, parce qu’il était irrité.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Il s’élevait de la fumée dans ses narines, Et un feu dévorant sortait de sa bouche: Il en jaillissait des charbons embrasés.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
Il abaissa les cieux, et il descendit: Il y avait une épaisse nuée sous ses pieds.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
Il était monté sur un chérubin, et il volait, Il planait sur les ailes du vent.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
Il faisait des ténèbres sa retraite, sa tente autour de lui, Il était enveloppé des eaux obscures et de sombres nuages.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
De la splendeur qui le précédait s’échappaient les nuées, Lançant de la grêle et des charbons de feu.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
L’Éternel tonna dans les cieux, Le Très-Haut fit retentir sa voix, Avec la grêle et les charbons de feu.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
Il lança ses flèches et dispersa mes ennemis, Il multiplia les coups de la foudre et les mit en déroute.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
Le lit des eaux apparut, Les fondements du monde furent découverts, Par ta menace, ô Éternel! Par le bruit du souffle de tes narines.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
Il étendit sa main d’en haut, il me saisit, Il me retira des grandes eaux;
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
Il me délivra de mon adversaire puissant, De mes ennemis qui étaient plus forts que moi.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
Ils m’avaient surpris au jour de ma détresse; Mais l’Éternel fut mon appui.
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
Il m’a mis au large, Il m’a sauvé, parce qu’il m’aime.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
L’Éternel m’a traité selon ma droiture, Il m’a rendu selon la pureté de mes mains;
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
Car j’ai observé les voies de l’Éternel, Et je n’ai point été coupable envers mon Dieu.
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
Toutes ses ordonnances ont été devant moi, Et je ne me suis point écarté de ses lois.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
J’ai été sans reproche envers lui, Et je me suis tenu en garde contre mon iniquité.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Aussi l’Éternel m’a rendu selon ma droiture, Selon la pureté de mes mains devant ses yeux.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
Avec celui qui est bon tu te montres bon, Avec l’homme droit tu agis selon la droiture,
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
Avec celui qui est pur tu te montres pur, Et avec le pervers tu agis selon sa perversité.
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
Tu sauves le peuple qui s’humilie, Et tu abaisses les regards hautains.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
Oui, tu fais briller ma lumière; L’Éternel, mon Dieu, éclaire mes ténèbres.
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
Avec toi je me précipite sur une troupe en armes, Avec mon Dieu je franchis une muraille.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
Les voies de Dieu sont parfaites, La parole de l’Éternel est éprouvée; Il est un bouclier pour tous ceux qui se confient en lui.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
Car qui est Dieu, si ce n’est l’Éternel; Et qui est un rocher, si ce n’est notre Dieu?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
C’est Dieu qui me ceint de force, Et qui me conduit dans la voie droite.
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
Il rend mes pieds semblables à ceux des biches, Et il me place sur mes lieux élevés.
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Il exerce mes mains au combat, Et mes bras tendent l’arc d’airain.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
Tu me donnes le bouclier de ton salut, Ta droite me soutient, Et je deviens grand par ta bonté.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Tu élargis le chemin sous mes pas, Et mes pieds ne chancellent point.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
Je poursuis mes ennemis, je les atteins, Et je ne reviens pas avant de les avoir anéantis.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
Je les brise, et ils ne peuvent se relever; Ils tombent sous mes pieds.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
Tu me ceins de force pour le combat, Tu fais plier sous moi mes adversaires.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
Tu fais tourner le dos à mes ennemis devant moi, Et j’extermine ceux qui me haïssent.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
Ils crient, et personne pour les sauver! Ils crient à l’Éternel, et il ne leur répond pas!
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
Je les broie comme la poussière qu’emporte le vent, Je les foule comme la boue des rues.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Tu me délivres des dissensions du peuple; Tu me mets à la tête des nations; Un peuple que je ne connaissais pas m’est asservi.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
Ils m’obéissent au premier ordre, Les fils de l’étranger me flattent;
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
Les fils de l’étranger sont en défaillance, Ils tremblent hors de leurs forteresses.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
Vive l’Éternel, et béni soit mon rocher! Que le Dieu de mon salut soit exalté,
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
Le Dieu qui est mon vengeur, Qui m’assujettit les peuples,
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
Qui me délivre de mes ennemis! Tu m’élèves au-dessus de mes adversaires, Tu me sauves de l’homme violent.
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
C’est pourquoi je te louerai parmi les nations, ô Éternel! Et je chanterai à la gloire de ton nom.
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
Il accorde de grandes délivrances à son roi, Et il fait miséricorde à son oint, A David, et à sa postérité, pour toujours.