< Zabura 18 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
Jusqu'à la Fin. Pour David, serviteur de Dieu: il a composé au Seigneur les paroles de ce psaume le jour que le Seigneur l'a sauvé des mains de tous ses ennemis, et des mains de Saül, Et il a dit: Seigneur, je t'aimerai, toi qui es ma force.
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
Seigneur, mon appui, mon refuge et mon libérateur! Mon Dieu est mon champion, j'espèrerai en lui, il est mon défenseur, la force de mon salut; c'est lui qui me protège.
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
J'invoquerai le Seigneur en le louant, et je serai sauvé des mains de mes ennemis.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
Les angoisses de la mort m'ont environné; des torrents d'iniquités m'ont grandement troublé.
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol h7585)
J'étais investi par les tourments de l'enfer, j'avais été surpris par les filets de la mort. (Sheol h7585)
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
En ces afflictions, j'ai invoqué le Seigneur; j'ai crié vers mon Dieu: de sa demeure sainte il a entendu ma voix; mes cris arrivent jusqu'à lui, ils pénétreront dans ses oreilles.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
Et la terre a été ébranlée, elle a tremblé, et les assises des montagnes ont été troublées jusqu'en leurs fondements; et elles ont chancelé, parce que le Seigneur était courroucé contre eux.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Sa colère a fait jaillir de la fumée; et son visage a lancé sa flamme; des charbons en ont été embrasés.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
Il a incliné les cieux et il est descendu, et l'obscurité était sous ses pieds.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
Et il est monté sur les Chérubins, et il a volé; il a volé sur les ailes des vents;
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
Et il s'est entouré de ténèbres, et il y a fait son tabernacle dans l'eau sombre des nuées de l'air.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
Et les nuées ont passé devant lui, chassées par sa splendeur; il a lancé de la grêle et des charbons de feu.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
Et le Seigneur a tonné du haut du ciel; et le Très-Haut a fait entendre sa voix;
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
Et il a lancé ses flèches, et il a dispersé mes ennemis; il a multiplié les éclairs, et ils ont été troublés.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
Et les sources des eaux ont apparu, et les fondements de la terre ont été visibles, à cause de tes menaces, Seigneur, à cause du souffle de ta colère.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
Il a envoyé son secours du haut des cieux, et il m'a pris; il m'a retiré des abîmes de l'eau.
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
Il m'a sauvé de mes puissants ennemis et de ceux qui me haïssent; car ils étaient plus forts que moi.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
Ils m'ont pris au dépourvu le jour de mon affliction; mais le Seigneur a été mon appui.
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
Et il m'a conduit au large; il me sauvera, à cause de sa bonne volonté pour moi. [Il m'a sauvé de mes puissants ennemis et de ceux qui me haïssent.]
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
Et le Seigneur me récompensera selon ma justice, et selon la pureté de mes mains.
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
Car j'ai gardé les voies du Seigneur; je n'ai point été impie, m'écartant de mon Dieu.
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
J'ai eu présents à l'esprit tous ses jugements; et ses justices je ne les ai point éloignées de moi.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
Et je serai sans tache avec lui, et je me garderai de mon iniquité.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Et le Seigneur me récompensera selon ma justice, et selon la pureté de mes mains qui est manifeste à ses yeux.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
Avec le saint tu seras saint, ô Seigneur, et avec l'homme innocent, tu seras innocent.
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
Avec l'élu, tu seras élu, et avec le méchant tu seras impitoyable.
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
Et tu sauveras le peuple des humbles, et tu humilieras les yeux du superbe.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
Tu feras luire ma lampe. Seigneur mon Dieu, et tu éclaireras mes ténèbres.
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
Avec l'aide de mon Dieu je ne succomberai pas aux tentations, avec lui je franchirai le mur qui m'environne.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
O mon Dieu, ta voie est irréprochable; les paroles du Seigneur ont été éprouvées comme le feu; il est le protecteur de ceux qui espèrent en lui.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
Car qui est Dieu, sinon le Seigneur? qui est Dieu, sinon notre Dieu?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
C'est Dieu qui m'a ceint de force et qui a rendu ma voie sans tache.
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
C'est lui qui a donné à mes pieds l'agilité du cerf, et qui m'a établi sur les hauts lieux.
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
C'est lui qui a exercé mes mains aux combats, et qui a rendu mes bras forts comme un arc d'airain.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
Tu m'as accordé ta protection, pour mon salut; ta main droite m'a soutenu; tes châtiments ont réussi à me corriger; tes châtiments mêmes continueront de m'instruire.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Tu as élargi le chemin sous mes pas, et mes pieds n'ont point vacillé.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
Je poursuivrai mes ennemis, je les saisirai, je ne reviendrai pas qu'ils ne soient exterminés.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
Je les broierai, et ils ne pourront se soutenir; ils tomberont sous mes pieds.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
Et pour les combats tu m'as ceint de force; tu as abattu sous moi tous ceux qui s'étaient élevés contre moi.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
Et mes ennemis, tu leur as fait tourner le dos devant moi; et ceux qui me haïssaient, tu les as anéantis.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
Ils ont crié, mais il n'y avait là personne qui les sauvât; ils ont crié au Seigneur, et il ne les a pas exaucés.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
Je les briserai comme la poussière à la face du vent; je les balayerai comme la boue des places publiques.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Arrache-moi aux contradictions du peuple, tu me mettras à la tête des nations. Un peuple que je ne connaissais pas m'a été asservi;
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
Son oreille m'a entendu, et il m'a obéi. Des fils révoltés m'ont menti,
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
Des fils révoltés ont vieilli et ont boité, en sortant de leurs voies.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
Vive le Seigneur, béni soit le Seigneur mon Dieu, que le Dieu de mon salut soit exalté!
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
C'est toi, mon Dieu, qui te charges de mes vengeances; toi qui me soumets les peuples;
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
Toi, mon libérateur contre la colère de mes ennemis, tu m'élèveras au- dessus de ceux qui se sont révoltés contre moi; tu me délivreras de l'homme inique.
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
A cause de cela, Seigneur, je célébrerai ta gloire parmi les nations, et je chanterai ton nom.
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
Dieu exalte le salut de son roi; il est plein de miséricorde pour David son christ, et pour sa postérité dans les siècles des siècles.

< Zabura 18 >